• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Dace Kasashen Da Suka Ci Gaba Su Cika Alkawuran Da Suka Yi Game Da Sauyin Yanayi

by CGTN Hausa
2 years ago
Sauyin Yanayi

Yanzu haka kasashe da ragowar bangarorin da suka sanya hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD, na shirin hallara a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa, don gudanar da taro kan sauyin yanayi ko COP28, inda ake sa ran shugabannin kasashen duniya za su tattauna kan matsalolin dake hana ruwa gudu game da magance matsalar sauyin yanayi dake ci gaba da addabar sassan duniya ta fannoni daban-daban.

A taron da ya gudana a kasar Masar a bara, galibin shugabannin kasashen da suka gabatar da jawabai a taron, sun kara yin kira ne ga kasashe masu karfin tattalin arziki, da su dauki matakai na zahiri maimakon maganar fatar baki da suka saba yi a duk lokacin da aka kira irin wannan taro ko wani dandali mai kama da wannan, domin shawo kan illolin da sauyin yanayin ke haifarwa, kamar zafi da fari da ambaliyar ruwa da mahaukaciyar guguwa dake tafe da mamakon ruwan sama da makamantansu.
Haka kuma sun yi kashedin cewa, lokaci fa yana kurewa, kuma duk wani jan kafa kan wannan batu, babu abin da zai haifar illa haddasa asarar rayuka da dukiyoyi.

  • An Kammala Aikin Bututun Karkashin Ruwa Na Sabuwar Hanyar Sin Da Ta Ratsa Teku
  • Sin Na Ba Da Gudummawa Wajen Samar Da Abinci Da Tsarin Samar Da Kaya A Duniya

Wani rahoto da hukumar kula da makamashi ta MDD ta fitar na nuna cewa, a shekaru 8 dake tafe, ana iya cewa, duniya ta kama hanyar fuskantar zafi mafi tsanani a tarihi. Shin ina muka dosa? Hukumomin MDD gami da kungiyoyi masu zaman kansu ma, sun yi gargadin cewa, an samu karuwar matsalar karancin abinci mai gina jiki a cikin shirye-shiryen kula da abinci mai gina jiki a fadin yankin kahon Afirka, wannan ma wata alama ce ta matsalar sauyin yanayi, haka kuma mutane da dama sun rasa abubuwan rayuwa, da hanyoyin da za su iya magance wannan bala’i, sannan kuma sun dogara baki daya kan taimako don biyan bukatunsu na yau da kullum, matakin da zai iya kalubalantar farfadowar fari.

A yayin da ake shirin gudanar da taron COP28, wanda ke nufin zama karo na 28 na babban taron kasashen duniya kan tsarin sauyin yanayi na MDD a birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa, daga ranar 30 ga watan Nuwamba zuwa 12 ga watan Disamba, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya jaddada cewa, akwai bukatar shugabannin kasashen duniya da za su halarci taron na wannan mako, da su dakile ci gaban mummunan dumamar yanayi da ake fuskanta, kafin a shiga wani mummunan yanayi.

Kalamansa na zuwa ne, bayan da a karshen mako ya ganewa idonsa yadda curin dutsen kankara ke saurin narkewa a Antatika, saurin da ya ninka sau uku fiye da yadda ake gani a farkon shekarun 1990.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

Masana na cewa, yanzu haka, mummunan yanayi na zafi na karuwa fiye da kima, yayin da kankara ke raguwa ga kuma yanayi mai tsanani, kuma kowa ya san mafita. Tilas ne shugabanni su dauki mataki don takaita karuwar yanayin zafin duniya zuwa ma’aunin digirin Celcius 1.5, da kare mutane daga matsalar yanayi, da kawo karshen amfani da makamashin dangin kwal, mai da iskar gas dake gurbata muhalli.

Yanzu dai dabara ta rage ga mai shiga rijiya. Ko dai duniya ta mayar da hankali wajen daukar managartan matakan magance wannan matsala ko kuma duniya ta ci gaba da shiga hali na kunci sakamakon matsalar sauyin yanayi. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Ya Dace Kasashen Da Suka Ci Gaba Su Cika Alkawuran Da Suka Yi Game Da Sauyin Yanayi

Ministan Wajen Sin Ya Jaddada Shawarar Kafa Kasashe 2 A Matsayin Hanyar Warware Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.