• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiya Alhamis 25 ga wata ne a babban dakin wasan kwaikwayon kasar Sin da ke nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar, aka nuna wasan kwaikwayon wake-wake mai suna Romeo da Juliet, wanda mai tsara kide-kide na kasar Faransa Charles Francois Gounod ya samar da shi. Masu fasaha na Sin da Faransa sun nuna wasan mai kayatarwa ne cikin hadin gwiwa, wasan da ya kasance kyautar musamman ta murnar cika shekaru 60 da kulla huldar jakadanci a tsakanin kasashen 2.

Yayin da kasar Sin ke mu’amala da kasashen yammacin duniya, Faransa ta sha bamban sosai, inda ta zama ta farko tsakanin manyan kasashen yammacin duniya da suka kulla huldar diplomasiyya da jamhuriyar jama’ar kasar Sin a hukumance, kana ta zama ta farko tsakanin manyan kasashen yammacin duniya da suka kyautata hulda da Sin zuwa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare daga dukkan fannoni da kuma tattaunawa da Sin dangane da manyan tsare-tsare.

  • Ilimi A Dukkan Matakai A Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ya Kai Kololuwar Matsayi
  • Kayan Da Aka Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Alamta Babban Karfin Tattalin Arzikin Kasar

A yayin liyafar da aka gudanar ta murnar cika shekaru 60 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Faransa a daren jiya, shugabannin kasashen 2 sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo, inda shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, tarihin musamman na huldar da ke tsakanin Sin da Faransa ya samar da ruhin Sin da Faransa mai ‘yancin kai, fahimtar juna, yin hangen nesa, moriyar juna da samun nasara tare. Ya kuma gabatar da shawarwari 4 dangane da zurfafa hadin gwiwar kasashen 2 a nan gaba, wato wajibi ne Sin da Faransa su tsaya kan raya huldarsu da habaka yin mu’amalar al’adu da kara azama kan cudanyar al’umma da yin kirar raya duniya mai sassa daban daban kuma mai adalci da tsari da oda, da bunkasar tattalin arzikin duniya mai kunshe da kowa da amfanawa kowa, da kuma nacewa kan samun moriyar juna da nasara tare. Xi ya gabatar da wadannan shawarwari 4 ne domin neman kare muradun bai daya na Sin da Faransa, da kokarin kara sauke nauyi dake wuyansu tare a duniya, shawarwarin da suka tsara manufar raya huldar da ke tsakanin Sin da Faransa a shekaru 60 masu zuwa.

Sin da Faransa na da kujerun din din din a kwamitin sulhu na MDD, kuma kasashe ne masu kishin zaman lafiya da kin yarda da nuna kiyayya tsakanin rukunoni, da kuma rungumar manufar cudanyar sassa daban daban. A cikin duniyar da ke fama da tashin hankali, kamata ya yi Sin da Faransa su kara hada kansu, su daidaita matsalolin tafiyar da harkokin duniya tare, su kuma taimaka wajen kwantar da kura a duniya. (Tasallah Yuan)

 

Labarai Masu Nasaba

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: diflomasiyyaKungiyoyin Fararen HulaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Maido Da Huldar Diflomasiya Tsakanin Sin Da Nauru Ya Sake Tabbatar Da Matsaya Guda Uku Da Kasashen Duniya Suka Cimma

Next Post

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Related

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

2 hours ago
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

3 hours ago
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

4 hours ago
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”
Daga Birnin Sin

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

5 hours ago
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

6 hours ago
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao
Daga Birnin Sin

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

7 hours ago
Next Post
Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.