• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba EU Ta Dawo Daga Rakiyar Matakan Gurgunta Tsarin Cinikayya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Wajaba EU Ta Dawo Daga Rakiyar Matakan Gurgunta Tsarin Cinikayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da kiraye-kiraye da kasar Sin ta rika yi don gane da bukatar warware takaddamar cinikayya tsakaninta da kungiyar tarayyar Turai ta EU, hukumar gudanarwar kungiyar ta sanar da matakin kara harajin kaso 38.1 bisa dari, kan motoci masu amfani da lantarki kirar kasar Sin ko EVs da ake shigarwa kasashe mambobin kungiyar, matakin da ko shakka babu zai yi tarnaki ga kyakkyawar alakar raya tattalin arziki dake tsakanin Sin da EU.

Kafin sanar da matakin na EU dai, kungiyar ta yi zargin cewa kamfanonin kirar motoci samfurin EVs na kasar Sin na samun rangwame daga gwamnati, don haka EU ke ganin wajibi ne ta karawa sashen haraji domin cike gibin cinikayyar motocin.

  • Xi Jinping: Sin Za Ta Ci Gaba Da Kasancewa Cikin Rukunin Kasashe Masu Tasowa
  • Sojojin Nijeriya Sun Kashe Ƴan Bindigar Daji A Dajin Taraba, Sun Ƙwato Makamai Da Kayan Aiki

To sai dai masu fashin baki da dama na ganin wannan batu na kara haraji na da nasaba da siyasa, ba wai tsantsar harkar tattalin arziki ba ne. Hakan ne ma ya sanya, da yawa daga kamfanonin kirar motoci na Turai suka bayyana adawa da wannan anniya ta kara haraji kan motocin EVs kirar kasar Sin.

Kaza lika, a matsayinsu na manyan budaddun kasuwanni, kuma masu taka muhimmiyar rawa a fannin dunkulewar duniya, Sin da EU na da masana’antu, kuma suna rarraba hajojinsu zuwa sassan duniya daban daban, a wani yanayin dake hade da juna, ta yadda zai yi wuya a iya raba tsakanin hada-hadar da suka jima suna gudanarwa tare.

Ana iya ganin wannan alaka a sashen cinikayyar motoci tsakanin sassan biyu. Alal misali, motocin da ake kerawa a Turai na samun matukar karbuwa a kasuwannin Sin. Yayin da a daya hannun, kamfanonin kera motoci na Sin suka shafe tsawon shekaru suna zuba jari, da daga matsayin fasahohinsu na kirkire-kirkire, har suka kai matsayin shiga takara mai inganci a fannin samar da motoci samfurin EVs, wadanda kasuwarsu ke matukar habaka yanzu haka a Turai.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Don haka dai ya kamata bangaren EU ya yi karatun ta nutsu, ya yi watsi da matakai na kariyar cinikayya, domin aiwatar da hakan ba abun da zai haifar sai koma baya. Kuma wannan mataki da wasu tsirarun ’yan siyasar Turai ke yayatawa, zai jefa al’ummun kasashensu cikin mawuyacin halin tsadar hajoji a wannan fanni, da rage damar su ta more kyakkyawar rayuwa.

Har ila yau, matakin karin harajin zai iya nuna rashin tabbas game da manufar da EU ta ce tana kai, ta sauya akala zuwa ga samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi. Ya dace EU ta yi nazari sosai, ta sauya matsaya domin kaucewa “Haihuwar ‘Da Maras Ido”! (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BRICSEUNATO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Shirin EU Na Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Amfani Da Lantarki Kirar Sin Bai Samu Karbuwa Ba?

Next Post

Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

Related

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

19 hours ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

20 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

21 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

22 hours ago
EU
Daga Birnin Sin

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

23 hours ago
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000
Daga Birnin Sin

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

24 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

Tsadar Rayuwa A Babbar Sallah: Yadda Magidanta Ke Sama Wa Kansu Mafita

LABARAI MASU NASABA

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

September 9, 2025
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.