• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

by CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin baya, ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin ya fitar da rahoton shekarar 2023, game da keta hakkokin bil Adama dake wakana a kasar Amurka, wanda ya fallasa yanayin kara tabarbarewar hakkin bil Adama a kasar, inda aka gabatar da shaidu da alkaluma kan hakan.

Rahoton ya nuna yadda Amurkawa ke shan fama da matsaloli masu nasaba da keta hakkinsu na ’yan kasa da na siyasa, inda ’yan siyasar kasar ke watsi da alkawuran da suka dauka na kare martabar alumma, maimakon haka, ba abun da ake gani illa nuna wariyar launin fata, da koma bayan tattalin arziki da rashin daidaito, da keta hakkokin mata da yara kanana da sauransu. A daya hannun kuma yadda kasar ke aiwatar da manufofin baba-kere, da shiga sharo ba shanu sun kara haifar da matsalolin jin kai da tashe-tashen hankula a sassa daban daban na duniya.

  • Kasar Sin Na Hada Kai Da Kasa Da Kasa A Kokarin Inganta Muhallin Halittun Duniya
  • Mafarkin Amurka Ya Rube Saboda Tsanantar Gibin Dake Tsakanin Matalauta Da Masu Arziki  

Ko shakka babu lura da wadannan abubuwa na zahiri da Amurka ke fama da su, muna iya cewa kasar ta gaza wajen sauke nauyin alummunta na kare musu hakkokinsu.

Bisa alkaluman kididdiga, a kiyasin da aka yi a shekarar 2023 da ta gabata, adadin Amurkawa da aka hallaka ta hare-haren bindiga sun kai 43,000, adadin da ya kai kimanin mutum 117 ke nan a duk rana guda, baya ga a kalla mutane 1,247 da matakan amfani da karfin tuwo fiye da kima na ’yan sanda suka haifar da rasuwar su.

A bangaren tattalin arziki kuwa, gibin dake akwai tsakanin masu dukiya da matalauta a kasar ya kai matsayin koli a baya bayan nan, sama da yadda aka taba gani cikin shekaru masu tarin yawa.

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Sai dai duk da wannan matsaloli, masu nasa da gaza kare hakkokin bil Adama da Amurkawa ke fuskanta a cikin gida, ’yan siyasar kasar da gwamnati na kawar da kai, tare da yunkurin bankado wasu zarge-zarge da suke dorawa sauran sassan kasa da kasa. Ga misali, a baya bayan nan, maaikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da rahoton nazarin hakkokin bil Adama na shekarar 2023, mai kunshe da wai hali da kasashe da yankuna kusan 200 ke ciki game da kare hakkin dan Adam, amma abun mamaki shi ne babu wani bayani cikin rahoton, wanda ya yi tsokaci kan halin da ita kanta Amurka ke ciki a wannan fanni.

Tabbas, wannan yanayi ya yi kama da karin maganar bahaushe da kan ce Laifi tudu ne ka taka naka ka hango na wani. A zahiri Amurka ta nuna halayyarta ta danniya, da nuna fin karfi, da son kai da munafurci.

Masharhanta da dama na ganin duniya ta riga ta farka, alummunta suna iya gane inda aka dosa, kuma jamaa suna kara gane masu kaunar zaman lafiya, da masu son tada zaune-tsaye, kamar dai yadda hakan ya bayyana a fili yayin rikicin kasar Israila da alummar Falasdinawa da har yanzu ya ki ci ya ki cinyewa. Duniya ta ga yadda kasashe da dama masu son zama lafiya ke ta kiraye-kiraye na dakatar da wuta, da kawo karshen yaki, yayin da Amurka a nata bangare ta gaza amfani da tasirin ta domin goyawa wannan manufa baya, alamarin da karara ke nuni ga goyon bayan da take yiwa manufar keta hakkokin biladama.

Wajaba Amurka ta yiwa kanta alkalanci, ta sauka daga matsayin mai yin baki biyu, kuma a maimakon mai nuna yatsa ga sauran sassa kan batun kare hakkin bil Adama, kamata ya yi ta sauke nauyin dake wuyanta na goyon bayan wanzar da zaman lafiya a cikin gidanta, da ma a fagen kasa da kasa.

Kaza lika, ya zama wajibi ta dakatar da tsoma baki cikin harkokin sauran kasashe, ta kuma daina shiga harkokin sauran sassa dake bin nasu tsarin na kare hakkokin bil adama, kana ta sauka daga matsayin mai rura wutar yake da tashin hankali. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'adun SinawaAlakar Sin da AfirkaYakin Ukraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Zumunci A Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Yake Da Danko Matuka

Next Post

Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

Related

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

10 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

15 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

16 hours ago
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

17 hours ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

17 hours ago
Next Post
Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

LABARAI MASU NASABA

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.