• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin baya, ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin ya fitar da rahoton shekarar 2023, game da keta hakkokin bil Adama dake wakana a kasar Amurka, wanda ya fallasa yanayin kara tabarbarewar hakkin bil Adama a kasar, inda aka gabatar da shaidu da alkaluma kan hakan.

Rahoton ya nuna yadda Amurkawa ke shan fama da matsaloli masu nasaba da keta hakkinsu na ’yan kasa da na siyasa, inda ’yan siyasar kasar ke watsi da alkawuran da suka dauka na kare martabar alumma, maimakon haka, ba abun da ake gani illa nuna wariyar launin fata, da koma bayan tattalin arziki da rashin daidaito, da keta hakkokin mata da yara kanana da sauransu. A daya hannun kuma yadda kasar ke aiwatar da manufofin baba-kere, da shiga sharo ba shanu sun kara haifar da matsalolin jin kai da tashe-tashen hankula a sassa daban daban na duniya.

  • Kasar Sin Na Hada Kai Da Kasa Da Kasa A Kokarin Inganta Muhallin Halittun Duniya
  • Mafarkin Amurka Ya Rube Saboda Tsanantar Gibin Dake Tsakanin Matalauta Da Masu Arziki  

Ko shakka babu lura da wadannan abubuwa na zahiri da Amurka ke fama da su, muna iya cewa kasar ta gaza wajen sauke nauyin alummunta na kare musu hakkokinsu.

Bisa alkaluman kididdiga, a kiyasin da aka yi a shekarar 2023 da ta gabata, adadin Amurkawa da aka hallaka ta hare-haren bindiga sun kai 43,000, adadin da ya kai kimanin mutum 117 ke nan a duk rana guda, baya ga a kalla mutane 1,247 da matakan amfani da karfin tuwo fiye da kima na ’yan sanda suka haifar da rasuwar su.

A bangaren tattalin arziki kuwa, gibin dake akwai tsakanin masu dukiya da matalauta a kasar ya kai matsayin koli a baya bayan nan, sama da yadda aka taba gani cikin shekaru masu tarin yawa.

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

Sai dai duk da wannan matsaloli, masu nasa da gaza kare hakkokin bil Adama da Amurkawa ke fuskanta a cikin gida, ’yan siyasar kasar da gwamnati na kawar da kai, tare da yunkurin bankado wasu zarge-zarge da suke dorawa sauran sassan kasa da kasa. Ga misali, a baya bayan nan, maaikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da rahoton nazarin hakkokin bil Adama na shekarar 2023, mai kunshe da wai hali da kasashe da yankuna kusan 200 ke ciki game da kare hakkin dan Adam, amma abun mamaki shi ne babu wani bayani cikin rahoton, wanda ya yi tsokaci kan halin da ita kanta Amurka ke ciki a wannan fanni.

Tabbas, wannan yanayi ya yi kama da karin maganar bahaushe da kan ce Laifi tudu ne ka taka naka ka hango na wani. A zahiri Amurka ta nuna halayyarta ta danniya, da nuna fin karfi, da son kai da munafurci.

Masharhanta da dama na ganin duniya ta riga ta farka, alummunta suna iya gane inda aka dosa, kuma jamaa suna kara gane masu kaunar zaman lafiya, da masu son tada zaune-tsaye, kamar dai yadda hakan ya bayyana a fili yayin rikicin kasar Israila da alummar Falasdinawa da har yanzu ya ki ci ya ki cinyewa. Duniya ta ga yadda kasashe da dama masu son zama lafiya ke ta kiraye-kiraye na dakatar da wuta, da kawo karshen yaki, yayin da Amurka a nata bangare ta gaza amfani da tasirin ta domin goyawa wannan manufa baya, alamarin da karara ke nuni ga goyon bayan da take yiwa manufar keta hakkokin biladama.

Wajaba Amurka ta yiwa kanta alkalanci, ta sauka daga matsayin mai yin baki biyu, kuma a maimakon mai nuna yatsa ga sauran sassa kan batun kare hakkin bil Adama, kamata ya yi ta sauke nauyin dake wuyanta na goyon bayan wanzar da zaman lafiya a cikin gidanta, da ma a fagen kasa da kasa.

Kaza lika, ya zama wajibi ta dakatar da tsoma baki cikin harkokin sauran kasashe, ta kuma daina shiga harkokin sauran sassa dake bin nasu tsarin na kare hakkokin bil adama, kana ta sauka daga matsayin mai rura wutar yake da tashin hankali. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'adun SinawaAlakar Sin da AfirkaYakin Ukraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Zumunci A Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Yake Da Danko Matuka

Next Post

Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

Related

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

56 minutes ago
An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

2 hours ago
Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

3 hours ago
Xi: Ana Kokarin Rubuta Sabon Babi Na Zamanantar Da Sin A Lardin Shanxi
Daga Birnin Sin

Xi: Ana Kokarin Rubuta Sabon Babi Na Zamanantar Da Sin A Lardin Shanxi

3 hours ago
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

23 hours ago
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

24 hours ago
Next Post
Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

LABARAI MASU NASABA

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

July 8, 2025
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

July 8, 2025
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

July 8, 2025
An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

July 8, 2025
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

July 8, 2025
Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

July 8, 2025
Xi: Ana Kokarin Rubuta Sabon Babi Na Zamanantar Da Sin A Lardin Shanxi

Xi: Ana Kokarin Rubuta Sabon Babi Na Zamanantar Da Sin A Lardin Shanxi

July 8, 2025
Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello

Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello

July 8, 2025
Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

July 8, 2025
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.