ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauya Matsaya Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

A ’yan kwanakin baya, ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin ya fitar da rahoton shekarar 2023, game da keta hakkokin bil Adama dake wakana a kasar Amurka, wanda ya fallasa yanayin kara tabarbarewar hakkin bil Adama a kasar, inda aka gabatar da shaidu da alkaluma kan hakan.

Rahoton ya nuna yadda Amurkawa ke shan fama da matsaloli masu nasaba da keta hakkinsu na ’yan kasa da na siyasa, inda ’yan siyasar kasar ke watsi da alkawuran da suka dauka na kare martabar alumma, maimakon haka, ba abun da ake gani illa nuna wariyar launin fata, da koma bayan tattalin arziki da rashin daidaito, da keta hakkokin mata da yara kanana da sauransu. A daya hannun kuma yadda kasar ke aiwatar da manufofin baba-kere, da shiga sharo ba shanu sun kara haifar da matsalolin jin kai da tashe-tashen hankula a sassa daban daban na duniya.

  • Kasar Sin Na Hada Kai Da Kasa Da Kasa A Kokarin Inganta Muhallin Halittun Duniya
  • Mafarkin Amurka Ya Rube Saboda Tsanantar Gibin Dake Tsakanin Matalauta Da Masu Arziki  

Ko shakka babu lura da wadannan abubuwa na zahiri da Amurka ke fama da su, muna iya cewa kasar ta gaza wajen sauke nauyin alummunta na kare musu hakkokinsu.

ADVERTISEMENT

Bisa alkaluman kididdiga, a kiyasin da aka yi a shekarar 2023 da ta gabata, adadin Amurkawa da aka hallaka ta hare-haren bindiga sun kai 43,000, adadin da ya kai kimanin mutum 117 ke nan a duk rana guda, baya ga a kalla mutane 1,247 da matakan amfani da karfin tuwo fiye da kima na ’yan sanda suka haifar da rasuwar su.

A bangaren tattalin arziki kuwa, gibin dake akwai tsakanin masu dukiya da matalauta a kasar ya kai matsayin koli a baya bayan nan, sama da yadda aka taba gani cikin shekaru masu tarin yawa.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Sai dai duk da wannan matsaloli, masu nasa da gaza kare hakkokin bil Adama da Amurkawa ke fuskanta a cikin gida, ’yan siyasar kasar da gwamnati na kawar da kai, tare da yunkurin bankado wasu zarge-zarge da suke dorawa sauran sassan kasa da kasa. Ga misali, a baya bayan nan, maaikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da rahoton nazarin hakkokin bil Adama na shekarar 2023, mai kunshe da wai hali da kasashe da yankuna kusan 200 ke ciki game da kare hakkin dan Adam, amma abun mamaki shi ne babu wani bayani cikin rahoton, wanda ya yi tsokaci kan halin da ita kanta Amurka ke ciki a wannan fanni.

Tabbas, wannan yanayi ya yi kama da karin maganar bahaushe da kan ce Laifi tudu ne ka taka naka ka hango na wani. A zahiri Amurka ta nuna halayyarta ta danniya, da nuna fin karfi, da son kai da munafurci.

Masharhanta da dama na ganin duniya ta riga ta farka, alummunta suna iya gane inda aka dosa, kuma jamaa suna kara gane masu kaunar zaman lafiya, da masu son tada zaune-tsaye, kamar dai yadda hakan ya bayyana a fili yayin rikicin kasar Israila da alummar Falasdinawa da har yanzu ya ki ci ya ki cinyewa. Duniya ta ga yadda kasashe da dama masu son zama lafiya ke ta kiraye-kiraye na dakatar da wuta, da kawo karshen yaki, yayin da Amurka a nata bangare ta gaza amfani da tasirin ta domin goyawa wannan manufa baya, alamarin da karara ke nuni ga goyon bayan da take yiwa manufar keta hakkokin biladama.

Wajaba Amurka ta yiwa kanta alkalanci, ta sauka daga matsayin mai yin baki biyu, kuma a maimakon mai nuna yatsa ga sauran sassa kan batun kare hakkin bil Adama, kamata ya yi ta sauke nauyin dake wuyanta na goyon bayan wanzar da zaman lafiya a cikin gidanta, da ma a fagen kasa da kasa.

Kaza lika, ya zama wajibi ta dakatar da tsoma baki cikin harkokin sauran kasashe, ta kuma daina shiga harkokin sauran sassa dake bin nasu tsarin na kare hakkokin bil adama, kana ta sauka daga matsayin mai rura wutar yake da tashin hankali. (Saminu Alhassan)

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
Daga Birnin Sin

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Next Post
Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

Mayaƙan ISWAP Da Boko Haram 4 Sun Tuba Sun Miƙa Wuya A Borno

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.