• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Sin Da Amurka Su Gina Alaka Da Juna Karkashin Salon Martaba Juna Da Daidaito

by CMG Hausa
2 years ago
Amurka

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ya zama wajibi kasashen Sin da Amurka su gina alaka bisa salon martaba juna da daidaito, da girmama bambance-bambancensu na tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa da hanyoyin ci gaba. Kaza lika ya wajaba sassan biyu su kare moriya, da manyan abubuwan da ke jan hankalin su.

Wang Wenbin, wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya ce wasu rahotanni sun ruwaito cewa, a ranar Laraba, fadar White House ta Amurka ta shaidawa manema labarai shirin sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken, na ziyartar kasar Sin, inda aka bayyana cewa, Amurka na aiwatar da manufofin cudanya da kasar Sin masu dorewa, wato salon dangantakar sassan biyu yana kunshe da takara ba wai neman tashin hankali, fito-na-fito, ko sabon salon cacar baka ba.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Gimama Mabambantan Wayewar Kai Ta Bil Adama

Kaza lika Amurka na fatan ci gaba da gudanar da takara mai tsafta. Za ta kuma yi kokarin daidaita yanayin takara tare da Sin, da kuma bunkasa hadin gwiwa kan batutuwan da suka dace da burikan su.

Da yake amsa tambayar da aka yi masa kan wannan batu, Wang Wenbin ya ce shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sha nanata cewa, bai dace alakar Sin da Amurka ta zama ta idan bangare daya ya samu dayan ya yi asara ba, maimakon haka, dacewa ya yi sassan biyu su rika cimma nasara tare, ta yadda kowa zai iya samun riba ko hasara.

Ya ce ya kamata Sin da Amurka su rika kallon juna a matsayin abokan tafiya, a manufofin su na gida da na waje, da aiwatar da manyan tsare-tsare bisa ka’idoji, da nacewa martaba juna, da tafiya tare, bisa zaman lafiya da hadin gwiwar cimma moriyar juna. Kana su lalubo hanya mafi dacewa ta kyautata jituwa tsakanin su. Hakan ne zai kare moriyar su, da ma irin fata da sassan kasa da kasa ke yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

A wani ci gaban kuma, kamfanin tsaron yanar gizo na Amurka mai suna “Mandiant Corporation”, ya fitar da wata sanarwa a baya-bayan nan, wadda a cikin ta ya ce, yana zargin kasar Sin da baiwa wasu masu kutsen yanar gizo goyon baya, inda suka yi kutse cikin daruruwan na’urori masu kwakwalwa na gwamnati, da na sassa masu zaman kan su dake kasashe daban daban.

Da yake amsa tambaya game da hakan, Wang Wenbin ya ce da ma wannan kamfani ya sha fitar da irin wadannan rahotanni na karya, game da wadanda yake kira da wai “masu kutsen yanar gizo na Sin”, kuma abubuwan dake kunshe cikin rahoton kamfanin ba kamshin gaskiya ko kwarewar aiki a cikin su. (Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Next Post
Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar ‘Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar 'Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.