ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Ƙaddamar Da Manyan Ayyukan Tituna A Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
ayyuka

A ranar Juma’ar nan ne Gusau babban birnin Jihar Zamfara ta ƙara samun tagomashi yayin da tsohon Gwamnan Bauchi, Ahmed Adamu Mu’azu ya ƙaddamar da wasu ayyukan tituna da Gwamnatin Dauda Lawal ta kammala cikin shekara guda da karɓar mulki.

Alhaji Ahmed Adamu Mu’azu wanda yake tsohon Shugaban PDP na ƙasa, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa ayyukan inganta tituna da yake aiwatarwa.

Mai magana da yawun Gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa titunan da Adamu Mu’azu ya ƙaddamar, sun haɗa da titin Freedom Square zuwa mahaɗar Nasiha Chemist; sai kuma wacce ta tashi daga Freedom Square zuwa gidan gwamnati; da kuma ta gidan gwamnati zuwa Lalan zuwa Gada Biyu.

ADVERTISEMENT

ayyuka

Idris ya ƙara da cewa ayyukan titunan Freedom Square zuwa mahaɗar Nasiha Chemist, da ta Freedom Square zuwa gidan gwamnati, kamfanin Ronches Nigeria Limited ne ya aiwatar da su; sannan shi kuma kamfanin Triacta Nigeria Limited ya aiwatar da titin da ya tashi daga gidan gwamnati zuwa Lalan zuwa Gada-Biyu.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

Cikin jawabinsa wajen bikin, Gwamna Dauda Lawal ya bugi ƙirjin cewa tun da aka kafa jihar Zamfara, shekaru 28 ke nan, sai yanzu ne Gusau ta cancanci a kirata babban birnin jihar.

“Zan fara da yi wa babban baƙon mu marhabin lale zuwa wannan biki. Wannan kuwa ba wani ba ne illa Tshohon Gwamnan jihar Bauchi, kuma Tshohon Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, mai girma Alhaji Ahmad Adamu Mu’azu, CON. Har gobe abubuwan da ka kafa a matsayin ka na Gwamna da shugaban PDP, zai zama abin koyi ga shugabanni masu tasowa.

ayyuka

“Babu shakka, dole ne mu yi wa Allah godiya mara iyaka bisa damar da ya ba mu na aiwatar da ayyuka, uwa-uba, Allah ya ba mu damar cika alƙawuran Zamfarawa da muka ɗauka a lokacin yaƙin nemam zaɓe. Ina ƙara jaddada aniyata ta sadaukarwa ga jihata a kowane lokaci.

“Don haka, bisa waɗannan ni’imomi na Allah, yau za mu buɗe hanyar da ta tashi daga Freedom Square zuwa mahaɗar Nasiha Chemist, Freedom Square zuwa gidan gwamnati, wanda kamfanin Ronches Nigeria Limited ya aiwatar; sannan daga gidan gwamnati zuwa Lalan Gada-Biyu, shi kuma kamfanin Triacta Nigeria Limited ne ya aiwatar. Waɗannan na ciki wasu ayyukan da gwamnatina ta aiwatar daga lokacin da muka hau mulki.

“Waɗannan ayyuka da muke ƙaddamarwa a yau, kashi na biyu ne a jerin ayyukan mu masu ɗimbin yawa. Da zarar mun kammala tsare-tsaren da muka yi na raya birane, to dukkan mu za mu iya bugun ƙirji mu kira Gusau a matsayin babban birnin jihar mu. Bugu da ƙari, za mu aiwatar da ayyukan more rayuwa a duk Ƙananan Hukumomin jihar nan 14.

ayyuka

“Da wannan ɗan taƙaitaccen jawabin, na ke farin cikin gayyatar Tsohon Gwamnan jihar Bauchi, Alhaji Ahmad Adamu Mu’azu, CON, ya zo ya buɗe waɗannan ayyukan da gwamnatina ta aiwatar a shekara ɗaya da na yi ina shugabantar jihar nan, a matsayin wani sashe na ayyukan raya birane.”

Tun farko, Babban baƙo, Tsohon Gwamnan jihar Bauch, Alhaji Ahmad Adamu Mua’azu, CON, ya nuna matuƙar jin daɗin sa bisa waɗannan ayyukan na Gwamna Lawal, yana mai bayyana cewa shi shugaba ne mai ƙwazo da hangen nesa.

“A yau, ina mai alfahari da godiya ga Allah bisa ayyukan yabawa da Gwamna Dauda Lawal ya aiwatar.

“Babban al’amari na waɗannan titunan shi ne cewa an gina su da inganci kuma bisa tsarin yadda duniya ke tafiya. Zan iya tabbatar muku da cewa waɗannan hanyoyi ne masu ɗorewa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
Next Post
Laifukan Shafin Intanet Na Ci Gaba Da Ci Wa ‘Yan Nijeriya Tuwo A Kwarya

Laifukan Shafin Intanet Na Ci Gaba Da Ci Wa 'Yan Nijeriya Tuwo A Kwarya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.