• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Ƙaddamar Da Manyan Ayyukan Tituna A Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Yadda Aka Ƙaddamar Da Manyan Ayyukan Tituna A Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’ar nan ne Gusau babban birnin Jihar Zamfara ta ƙara samun tagomashi yayin da tsohon Gwamnan Bauchi, Ahmed Adamu Mu’azu ya ƙaddamar da wasu ayyukan tituna da Gwamnatin Dauda Lawal ta kammala cikin shekara guda da karɓar mulki.

Alhaji Ahmed Adamu Mu’azu wanda yake tsohon Shugaban PDP na ƙasa, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa ayyukan inganta tituna da yake aiwatarwa.

Mai magana da yawun Gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa titunan da Adamu Mu’azu ya ƙaddamar, sun haɗa da titin Freedom Square zuwa mahaɗar Nasiha Chemist; sai kuma wacce ta tashi daga Freedom Square zuwa gidan gwamnati; da kuma ta gidan gwamnati zuwa Lalan zuwa Gada Biyu.

ayyuka

Idris ya ƙara da cewa ayyukan titunan Freedom Square zuwa mahaɗar Nasiha Chemist, da ta Freedom Square zuwa gidan gwamnati, kamfanin Ronches Nigeria Limited ne ya aiwatar da su; sannan shi kuma kamfanin Triacta Nigeria Limited ya aiwatar da titin da ya tashi daga gidan gwamnati zuwa Lalan zuwa Gada-Biyu.

Labarai Masu Nasaba

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

Cikin jawabinsa wajen bikin, Gwamna Dauda Lawal ya bugi ƙirjin cewa tun da aka kafa jihar Zamfara, shekaru 28 ke nan, sai yanzu ne Gusau ta cancanci a kirata babban birnin jihar.

“Zan fara da yi wa babban baƙon mu marhabin lale zuwa wannan biki. Wannan kuwa ba wani ba ne illa Tshohon Gwamnan jihar Bauchi, kuma Tshohon Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, mai girma Alhaji Ahmad Adamu Mu’azu, CON. Har gobe abubuwan da ka kafa a matsayin ka na Gwamna da shugaban PDP, zai zama abin koyi ga shugabanni masu tasowa.

ayyuka

“Babu shakka, dole ne mu yi wa Allah godiya mara iyaka bisa damar da ya ba mu na aiwatar da ayyuka, uwa-uba, Allah ya ba mu damar cika alƙawuran Zamfarawa da muka ɗauka a lokacin yaƙin nemam zaɓe. Ina ƙara jaddada aniyata ta sadaukarwa ga jihata a kowane lokaci.

“Don haka, bisa waɗannan ni’imomi na Allah, yau za mu buɗe hanyar da ta tashi daga Freedom Square zuwa mahaɗar Nasiha Chemist, Freedom Square zuwa gidan gwamnati, wanda kamfanin Ronches Nigeria Limited ya aiwatar; sannan daga gidan gwamnati zuwa Lalan Gada-Biyu, shi kuma kamfanin Triacta Nigeria Limited ne ya aiwatar. Waɗannan na ciki wasu ayyukan da gwamnatina ta aiwatar daga lokacin da muka hau mulki.

“Waɗannan ayyuka da muke ƙaddamarwa a yau, kashi na biyu ne a jerin ayyukan mu masu ɗimbin yawa. Da zarar mun kammala tsare-tsaren da muka yi na raya birane, to dukkan mu za mu iya bugun ƙirji mu kira Gusau a matsayin babban birnin jihar mu. Bugu da ƙari, za mu aiwatar da ayyukan more rayuwa a duk Ƙananan Hukumomin jihar nan 14.

ayyuka

“Da wannan ɗan taƙaitaccen jawabin, na ke farin cikin gayyatar Tsohon Gwamnan jihar Bauchi, Alhaji Ahmad Adamu Mu’azu, CON, ya zo ya buɗe waɗannan ayyukan da gwamnatina ta aiwatar a shekara ɗaya da na yi ina shugabantar jihar nan, a matsayin wani sashe na ayyukan raya birane.”

Tun farko, Babban baƙo, Tsohon Gwamnan jihar Bauch, Alhaji Ahmad Adamu Mua’azu, CON, ya nuna matuƙar jin daɗin sa bisa waɗannan ayyukan na Gwamna Lawal, yana mai bayyana cewa shi shugaba ne mai ƙwazo da hangen nesa.

“A yau, ina mai alfahari da godiya ga Allah bisa ayyukan yabawa da Gwamna Dauda Lawal ya aiwatar.

“Babban al’amari na waɗannan titunan shi ne cewa an gina su da inganci kuma bisa tsarin yadda duniya ke tafiya. Zan iya tabbatar muku da cewa waɗannan hanyoyi ne masu ɗorewa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukaDauda LawalGusauƘaddamarwaTitunaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Nijeriya Ya Kirkiro Manjahar Wayar Salula Ta Biyan Kudade Ba Tare Da Intanet Ba

Next Post

Laifukan Shafin Intanet Na Ci Gaba Da Ci Wa ‘Yan Nijeriya Tuwo A Kwarya

Related

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
Labarai

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

1 hour ago
APC
Labarai

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

3 hours ago
Tinubu
Labarai

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

6 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

7 hours ago
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

10 hours ago
Next Post
Laifukan Shafin Intanet Na Ci Gaba Da Ci Wa ‘Yan Nijeriya Tuwo A Kwarya

Laifukan Shafin Intanet Na Ci Gaba Da Ci Wa 'Yan Nijeriya Tuwo A Kwarya

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.