• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gyara Kundin Tsarin Mulki Sau 5 Cikin Shekara 25

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Gyara

A cikin shekaru 25 da Nijeriya ta koma kan turbar dimokuradiyya, kundin tsarin mulki na shekara 1999 ya samu gyare-gyare guda 5 wanda ya lakume biliyoyin nairori kan kowani zama.

Wannan lamari ya sanya ayar tambaya game da ingancin aikin gyaran kundin tsarin mulkin kasar nan.

  • Majalisar Wakilai Ta Jinjina Wa Kamfanin Ɗangote Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa
  • Xi Ya Gana Da Shugabannin Majalisun Dokokin Kasashen Duniya

Gyara kundin tsarin mulki a Nijeriya yana tattare da wasu abubuwa, inda a hannu guda a kan iya cusa sabbin abubuwa masu muhimmanci, yayin da a bangare daya kuma aka saka wasu abubuwa marasa amfani.

A cewar wani bincike da Jaridar Banguard ta yi, sau biyar ana gyara kundin tsarin mulkin kasa nan, an gyara sau biyu a shekarar 2010 a karkashin shugaba Umaru Yar’Adua, sannan an gyara sau uku a karkashin shugaba Muhammadu Buhari.

Tun a watan Mayun shekarar 2006 ne aka yi watsi da shirin sake duba kundin tsarin mulkin kasar a karkashin shugaba Obasanjo, bisa zarginsa da neman wa’adi na uku.

LABARAI MASU NASABA

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

A nasa bangaren, tsohon shugaban kasa Jonathan, ya ki amincewa da kudirin gyara kundin tsarin mulkin kasar a shekarar 2015 da kuma karin dalilan yin hakan a wata wasika mai shafuka bakwai da aka karanta a zauren majalisar dattawa a ranar 15 ga Afrilu, 2015.

Sannan tsohon shugaban ya ce ba zai iya sanya hannu a kan sabbin shawarwarin da za su zama doka ba saboda rashin bin ka’ida da kuma yunkurin ‘yan majalisar na karya akidar raba madafun iko.

Daga cikin sauye-sauyen kundin tsarin mulki da aka sanya wa hannu a shekarar 2010, tsohon shugaban kasa ‘Yar’Adua ya saka hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) cikin asusun rabon tattalin arzikin kudi na tarayya.

Haka zalika, an mika wannan lamari ga majalisar dokoki ta kasa da ma’aikatar shari’a ta tarayya.

An rage shekarun cancantar shugabancin hukumar INEC daga shekaru 50 zuwa 40, sannan an rage na kwamishinonin zabe na kasa daga shekaru 40 zuwa 35.

Sannan kuma a lokacin ne aka rage adadin alkalan kotunan kararrakin zabe daga biyar zuwa uku, an gabatar da karar zaben gwamna ta kare a kotun koli maimakon kotun daukaka kara inda a da take karewa kafin 2011. Haka kuma an bi wa karar zabe wa’adin kwanaki 180 a kotun sauraren kararrakin zabe da kuma kwanaki 60 kowanne a kotun daukaka kara da kotun koli. Har ila yau, a cikin gyaran tsarin mulki na 2010 ne kotun masana’antu ta kasa ta zama babbar kotun mai cikakken ‘yanci.

A ranar 31 ga watan Mayun 2018 ne tsohon shugaba kasa Buhari ya rattaba hannu kan kudirin dokar bai wa matasa daman yin takara, wanda ya rage shekarun wasu mukaman siyasa ya zama doka.

Shekarun mukaman siyasan sun hada da na shugaban kasa daga shekara 40 zuwa 35, majalisar wakilai da na jiha daga shekaru 30 zuwa 25.

A ranar 8 ga watan Yuni, 2018, Buhari ya rattaba hannu kan wasu kudurorin doka har guda hudu na sauya kundin tsarin mulkin kasar.

Kudurorin sun hada da gyaran kundin tsarin mulki mai lamba 21 wanda ya shafi tantance al’amuran da suka shafi zaben.

Ya rage rana da lokacin tantance al’amuran da suka shafi tunkarar zabe, domin tabbatar da cewa al’amuran gabanin zaben a kotu ba su shiga lokacin zaben ba.

Yayin da aka kashe biliyoyin nairori kan wannan lamari na gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya, masu ruwa da tsaki sun ce tafiyar hawainiyar da ake yi na kawo cikas ga gyaran tsarin mulki wajen daidaita yanayin da ake ciki da kuma magance kalubalen da ke kunno kai.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba
Labarai

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Next Post
Wakilin Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Yi Kokarin Sa Kaimi Ga Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Batun Ukraine

Wakilin Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Yi Kokarin Sa Kaimi Ga Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Batun Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.