• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gyara Kundin Tsarin Mulki Sau 5 Cikin Shekara 25

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Yadda Aka Gyara Kundin Tsarin Mulki Sau 5 Cikin Shekara 25
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin shekaru 25 da Nijeriya ta koma kan turbar dimokuradiyya, kundin tsarin mulki na shekara 1999 ya samu gyare-gyare guda 5 wanda ya lakume biliyoyin nairori kan kowani zama.

Wannan lamari ya sanya ayar tambaya game da ingancin aikin gyaran kundin tsarin mulkin kasar nan.

  • Majalisar Wakilai Ta Jinjina Wa Kamfanin Ɗangote Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa
  • Xi Ya Gana Da Shugabannin Majalisun Dokokin Kasashen Duniya

Gyara kundin tsarin mulki a Nijeriya yana tattare da wasu abubuwa, inda a hannu guda a kan iya cusa sabbin abubuwa masu muhimmanci, yayin da a bangare daya kuma aka saka wasu abubuwa marasa amfani.

A cewar wani bincike da Jaridar Banguard ta yi, sau biyar ana gyara kundin tsarin mulkin kasa nan, an gyara sau biyu a shekarar 2010 a karkashin shugaba Umaru Yar’Adua, sannan an gyara sau uku a karkashin shugaba Muhammadu Buhari.

Tun a watan Mayun shekarar 2006 ne aka yi watsi da shirin sake duba kundin tsarin mulkin kasar a karkashin shugaba Obasanjo, bisa zarginsa da neman wa’adi na uku.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

A nasa bangaren, tsohon shugaban kasa Jonathan, ya ki amincewa da kudirin gyara kundin tsarin mulkin kasar a shekarar 2015 da kuma karin dalilan yin hakan a wata wasika mai shafuka bakwai da aka karanta a zauren majalisar dattawa a ranar 15 ga Afrilu, 2015.

Sannan tsohon shugaban ya ce ba zai iya sanya hannu a kan sabbin shawarwarin da za su zama doka ba saboda rashin bin ka’ida da kuma yunkurin ‘yan majalisar na karya akidar raba madafun iko.

Daga cikin sauye-sauyen kundin tsarin mulki da aka sanya wa hannu a shekarar 2010, tsohon shugaban kasa ‘Yar’Adua ya saka hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) cikin asusun rabon tattalin arzikin kudi na tarayya.

Haka zalika, an mika wannan lamari ga majalisar dokoki ta kasa da ma’aikatar shari’a ta tarayya.

An rage shekarun cancantar shugabancin hukumar INEC daga shekaru 50 zuwa 40, sannan an rage na kwamishinonin zabe na kasa daga shekaru 40 zuwa 35.

Sannan kuma a lokacin ne aka rage adadin alkalan kotunan kararrakin zabe daga biyar zuwa uku, an gabatar da karar zaben gwamna ta kare a kotun koli maimakon kotun daukaka kara inda a da take karewa kafin 2011. Haka kuma an bi wa karar zabe wa’adin kwanaki 180 a kotun sauraren kararrakin zabe da kuma kwanaki 60 kowanne a kotun daukaka kara da kotun koli. Har ila yau, a cikin gyaran tsarin mulki na 2010 ne kotun masana’antu ta kasa ta zama babbar kotun mai cikakken ‘yanci.

A ranar 31 ga watan Mayun 2018 ne tsohon shugaba kasa Buhari ya rattaba hannu kan kudirin dokar bai wa matasa daman yin takara, wanda ya rage shekarun wasu mukaman siyasa ya zama doka.

Shekarun mukaman siyasan sun hada da na shugaban kasa daga shekara 40 zuwa 35, majalisar wakilai da na jiha daga shekaru 30 zuwa 25.

A ranar 8 ga watan Yuni, 2018, Buhari ya rattaba hannu kan wasu kudurorin doka har guda hudu na sauya kundin tsarin mulkin kasar.

Kudurorin sun hada da gyaran kundin tsarin mulki mai lamba 21 wanda ya shafi tantance al’amuran da suka shafi zaben.

Ya rage rana da lokacin tantance al’amuran da suka shafi tunkarar zabe, domin tabbatar da cewa al’amuran gabanin zaben a kotu ba su shiga lokacin zaben ba.

Yayin da aka kashe biliyoyin nairori kan wannan lamari na gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya, masu ruwa da tsaki sun ce tafiyar hawainiyar da ake yi na kawo cikas ga gyaran tsarin mulki wajen daidaita yanayin da ake ciki da kuma magance kalubalen da ke kunno kai.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: majalisaNigeriaTsarin Mulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Kafofin Watsa Labaru Na “Abokan Afirka” A Beijing

Next Post

Wakilin Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Yi Kokarin Sa Kaimi Ga Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Batun Ukraine

Related

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

49 minutes ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

9 hours ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

10 hours ago
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

12 hours ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

14 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

15 hours ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Yi Kokarin Sa Kaimi Ga Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Batun Ukraine

Wakilin Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Yi Kokarin Sa Kaimi Ga Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Batun Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.