• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Bikin Kaddamar Da Littafin Babban Editan LEADERSHIP A Abuja

by Abubakar Abba
11 months ago
in Labarai
0
Yadda Aka Yi Bikin Kaddamar Da Littafin Babban Editan LEADERSHIP A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Larabar nan ne aka kaddamar da wani mashahurin littafi da Babban Edita kuma Babban Mataimakin Shugaban Rukunin Kamfanonin LEADERSHIP, Mista Azubuike Ishiekwene ne ya rubuta, mai taken “Rubutu don Kafafan Yada Labarai da mayar da shin a kudi”.

Taron ya gudana ne a babbar cibiyar tunawa da Shehu Musa ‘Yar’Aduwa da ke tsakiyar Babban Birnin Tarayya Abuja.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya

Da yake gabatar da jawabi, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mo-hammad Idris, ya bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta himmatu wajen tal-lafa wa aikin jarida bisa ‘yanci.

Idris wanda yake magana a matsayin shugaban taron ya bayyana cewa, ““Yayin da muke murnar wannan gagarumin buki, yana da kyau mu sake jaddada aniyar gwamna-tin Tinubu na samar da ‘yancin aikin jarida.

“Mun fahimci cewa al’umma za ta ci gaba ne kawai idan sassanta na kafafen yada laba-rai suka sami ‘yancin bayar da rahoton gaskiya ba tare da fargabar ladabtarwa ba, san-nan kuma ta rika hukunta masu rike da madafun iko,” inji Idris.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Ya yaba wa Ishiekwene a matsayin marubuci, edita, shugaban gudanarwa, mawallafi, mai ba da shawara, kuma abin koyi, inda ya bayyana matsayinsa na Babban Ma-taimakin Shugaban Rukunin Yada Labarai na LEADERSHIP a matsayin abin jinjina.

Idris ya yaba da littafin, inda ya bayyana shi a matsayin wani tsari na kasuwanci wanda ke cike gibin da ke tsakanin aiki da kasuwanci a bangaren yada labarai.

Ya lura cewa littafin yana da amfani ga masu karatu da yawa, ciki har da matasa da manya, masu zaman kansu, ko kuma masu cikakken aikin jarida.

Idris ya kuma yaba wa Ishiekwene bisa yadda ya tara fitattun jaruman kafafen yada lab-arai, mawallafa, editoci, malamai, da ‘yan jarida domin kaddamar da littafin.

Ministan ya kara da bayyana Ishiekwene a matsayin shugaba wanda ya jagoranci man-yan gidajen yada labarai da horar da matasa kwararru.

Ya jaddada cewa babban sha’awar Ishiekwene ya kasance a cikin rubutu, inda yake tsara bayanai na fahimta ga jama’a cikin haske sama da shekaru talatin.

Idris ya bayyana muhimmancin ‘yan jarida a matsayin ginshikin tsarin dimokuradiyya, yana mai jaddada cewa al’umma na samun bunkasuwa yayin da kafafen yada labaranta za su iya bayar da labarin gaskiya ba tare da tsoro ba tare da dora wa masu rike da ma-dafun iko alhakinsu na kula da jama’a.

Ita ma a nata bangaren, Shugabar Rukunin Kamfanonin LEADERSHIP, Zainab Nda-Isaiah, ta bayyana damuwarta kan yadda `yan jarida da marubuta ke fama da kamfar kudi da sukuni, duk kuwa da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen fito da ra’ayin jama’a da kawo sauyi a cikin al’umma.

Da take jawabi a wajen taron, ta jaddada rashin jin dadin halin da marubuta da yawa suke fuskanta na talauci duk da ayyukan da suke yi masu muhimmanci.

Ta yi imanin cewa littafin Ishiekwene zai ba da haske mai mahimmanci da kuma koyar aiki don taimakawa marubuta su guje wa cusa kai cikin duhu da wahalar samun kudi.

Zainab ta bayyana littafin a matsayin cikakken jagora wanda ba wai kawai ya shafi tsarin rubuce-rubuce ne ba har ma da jan hankali kan amfani da fasahar rubuce-rubuce wajen samun kudade.

Ta kuma yaba wa babban editan kuma babban mataimakin shugaban kamfanin LEADERSHIP Ishiekwene bisa jajircewarsa da sanin ya kamata, wanda hakan ya taimaka matuka wajen ci gaban littafin.

Da yake jawabin godiya, Mista Azubuike Ishiekwene ya nuna jin dadinsa bisa yadda aka amsa goron gayyatar bikin tare da jaddada cewa godiyarsa ba za ta misaltu ba.

Taron ya samu halartar manyan mutane irin su Sanata Ireti Heebah Kingibe, da mawallafin jaridaer Ban-guard Sam Amuka, da Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo, SAN, da tsohon kakakin shugaban kasa Dr. Reuben Abati, fitaccen marubucin jarida kuma mai gabatar da shirye-shiryen talabijin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LEADERSHIPLittafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

CGTN Ya Nuna Yadda Mutanen Asiya Ke Kallon Amurka

Next Post

Sin: Hada-hadar Sufuri Ta Bunkasa Cikin Watanni 5 Na Farkon Shekarar Bana

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

1 hour ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Sin: Hada-hadar Sufuri Ta Bunkasa Cikin Watanni 5 Na Farkon Shekarar Bana

Sin: Hada-hadar Sufuri Ta Bunkasa Cikin Watanni 5 Na Farkon Shekarar Bana

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.