ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Bikin Kaddamar Da Littafin Babban Editan LEADERSHIP A Abuja

by Abubakar Abba
2 years ago
Leadership

A ranar Larabar nan ne aka kaddamar da wani mashahurin littafi da Babban Edita kuma Babban Mataimakin Shugaban Rukunin Kamfanonin LEADERSHIP, Mista Azubuike Ishiekwene ne ya rubuta, mai taken “Rubutu don Kafafan Yada Labarai da mayar da shin a kudi”.

Taron ya gudana ne a babbar cibiyar tunawa da Shehu Musa ‘Yar’Aduwa da ke tsakiyar Babban Birnin Tarayya Abuja.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya

Da yake gabatar da jawabi, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mo-hammad Idris, ya bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta himmatu wajen tal-lafa wa aikin jarida bisa ‘yanci.

ADVERTISEMENT

Idris wanda yake magana a matsayin shugaban taron ya bayyana cewa, ““Yayin da muke murnar wannan gagarumin buki, yana da kyau mu sake jaddada aniyar gwamna-tin Tinubu na samar da ‘yancin aikin jarida.

“Mun fahimci cewa al’umma za ta ci gaba ne kawai idan sassanta na kafafen yada laba-rai suka sami ‘yancin bayar da rahoton gaskiya ba tare da fargabar ladabtarwa ba, san-nan kuma ta rika hukunta masu rike da madafun iko,” inji Idris.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Ya yaba wa Ishiekwene a matsayin marubuci, edita, shugaban gudanarwa, mawallafi, mai ba da shawara, kuma abin koyi, inda ya bayyana matsayinsa na Babban Ma-taimakin Shugaban Rukunin Yada Labarai na LEADERSHIP a matsayin abin jinjina.

Idris ya yaba da littafin, inda ya bayyana shi a matsayin wani tsari na kasuwanci wanda ke cike gibin da ke tsakanin aiki da kasuwanci a bangaren yada labarai.

Ya lura cewa littafin yana da amfani ga masu karatu da yawa, ciki har da matasa da manya, masu zaman kansu, ko kuma masu cikakken aikin jarida.

Idris ya kuma yaba wa Ishiekwene bisa yadda ya tara fitattun jaruman kafafen yada lab-arai, mawallafa, editoci, malamai, da ‘yan jarida domin kaddamar da littafin.

Ministan ya kara da bayyana Ishiekwene a matsayin shugaba wanda ya jagoranci man-yan gidajen yada labarai da horar da matasa kwararru.

Ya jaddada cewa babban sha’awar Ishiekwene ya kasance a cikin rubutu, inda yake tsara bayanai na fahimta ga jama’a cikin haske sama da shekaru talatin.

Idris ya bayyana muhimmancin ‘yan jarida a matsayin ginshikin tsarin dimokuradiyya, yana mai jaddada cewa al’umma na samun bunkasuwa yayin da kafafen yada labaranta za su iya bayar da labarin gaskiya ba tare da tsoro ba tare da dora wa masu rike da ma-dafun iko alhakinsu na kula da jama’a.

Ita ma a nata bangaren, Shugabar Rukunin Kamfanonin LEADERSHIP, Zainab Nda-Isaiah, ta bayyana damuwarta kan yadda `yan jarida da marubuta ke fama da kamfar kudi da sukuni, duk kuwa da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen fito da ra’ayin jama’a da kawo sauyi a cikin al’umma.

Da take jawabi a wajen taron, ta jaddada rashin jin dadin halin da marubuta da yawa suke fuskanta na talauci duk da ayyukan da suke yi masu muhimmanci.

Ta yi imanin cewa littafin Ishiekwene zai ba da haske mai mahimmanci da kuma koyar aiki don taimakawa marubuta su guje wa cusa kai cikin duhu da wahalar samun kudi.

Zainab ta bayyana littafin a matsayin cikakken jagora wanda ba wai kawai ya shafi tsarin rubuce-rubuce ne ba har ma da jan hankali kan amfani da fasahar rubuce-rubuce wajen samun kudade.

Ta kuma yaba wa babban editan kuma babban mataimakin shugaban kamfanin LEADERSHIP Ishiekwene bisa jajircewarsa da sanin ya kamata, wanda hakan ya taimaka matuka wajen ci gaban littafin.

Da yake jawabin godiya, Mista Azubuike Ishiekwene ya nuna jin dadinsa bisa yadda aka amsa goron gayyatar bikin tare da jaddada cewa godiyarsa ba za ta misaltu ba.

Taron ya samu halartar manyan mutane irin su Sanata Ireti Heebah Kingibe, da mawallafin jaridaer Ban-guard Sam Amuka, da Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo, SAN, da tsohon kakakin shugaban kasa Dr. Reuben Abati, fitaccen marubucin jarida kuma mai gabatar da shirye-shiryen talabijin.

Leadership
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Sin: Hada-hadar Sufuri Ta Bunkasa Cikin Watanni 5 Na Farkon Shekarar Bana

Sin: Hada-hadar Sufuri Ta Bunkasa Cikin Watanni 5 Na Farkon Shekarar Bana

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.