• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Cece-ku-ce Tsakanin Jaruma Adama Da Furodusa Isah Kan ₦200,000

by Zubairu M Lawal
10 months ago
in Nishadi
0
Yadda Aka Yi Cece-ku-ce Tsakanin Jaruma Adama Da Furodusa Isah Kan ₦200,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Furodusa a masana’antar shirya fina-finan Hausa na jihar Nasarawa, Isah Umar ya zargi Jaruma Adama Saleh Pantami (Adaman Kamaye) da gudar masa da kudin aiki har naira 200,000 da ya umurce ta ta bai wa jaruma Zahra Diamond.

Da yake zantawa da manema labarai, Furodusan ya ce; bayan da aka ba ta kuɗin ta bai wa Zahra Diamond da nufin ta zo aikin wani fim mai suna ‘Takaddama’, ita wacce aka gayyata ba ta zo ba, ita kuma Adama ba ta mayar masa da kudin ba.

  • Ban Taba Tunanin Fitowa A Cikin Fina-Finan Hausa Ba -Kamaye
  • Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim – Amina

Furodusan ya bayyana cewa ya ɓukaci lambar jaruma Zahra ne domin ta zo jihar Nasarawa wajen aikin fim ɗin, nan take Adaman ta ce ta santa kuma za ta kira ta.

Bayan sakar mata ragamar tattaunawa da jaruma Diamond, Adaman Kamaye ta ce sun shirya kan za a bata naira dubu 200, inda nan take ta umurci furodusan da ya ba ta kudin don ta tura mata.

Bayan Adaman ta kammala aikinta aka sallame ta tare da alkawarin cewa Zahra za ta zo gobe ko jibi amma shiru babu labari, daga bisani aka tuntubi Zahra Diamond inda ta bayyana cewa Adama ta kira ta a kan za ta yi aiki amma ta ce mata ba za ta iya zuwa ba saboda dalilai na tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Daga ƙarshe dai Furodusan ya zargi Adaman da cewa ta daina daukar wayarsa don jin inda kuɗinsa ya makale.
Labarin da ya janyo cece-kuce a masana’antar Fina-finan Hausa.

Sai dai kuma, da take mayar da martani kan zargin, Hajiya Adama Saleh Pantami, da ake wa laƙabi da Adaman Kamaye, ta ce; ita ba ta ci masa kudinsa ko kobo ba, hasali ma ya hada ta da lauyansa kuma sun warware komai da komai.

Da farko, ta ce ya gayyace ta aikin da aka ƙayyade za a yi a kwana huɗu ne, sai aka samu ƙarin kwana biyu a kai.

Bayan haka, Adama ta ce; na je da kayan saidawa kuma wanda ya gayyace ni aikin ya yi min ciniki na naira ₦285,000, da ya tashi biya sai aiko min da ₦240,000, ka ga saura ₦45,000.

A kashi na biyu kuma, ya yi min cinikin kaya na ₦257,000 sai ya ba ni ₦230,000, ya rage min ₦27,000. Sanan da ya buƙaci na kawo masa Zahra Diamond a matsayin jaruma da za ta yi aiki, ya bayar da ₦200,000 daga bisani Zahra Diamond ta ce ba za ta samu zuwa ba saboda gurin ya yi mata nisa.

“Dama kuɗin da ya ba ni na tura wa Zahra Diamond suna wajena ban tura mata ba. Sai na ce wa Salisu Mariri yaya batun ragowar kuɗin aikina da na kara kwanaki? Sai Mariri ya ce; kika san irin alherin da zai yi miki nan gaba? Sai na ce a’a aikin alheri daban na Sana’a daban. Duk abin da za a yi a yi da ƙa’ida. Ya ce; na yi haƙuri sai muka kamo hanya muka taho.”

To da ya nemi na dawo masa da kudin sai na ce ta yaya alhalin lissafin kuɗina (na sayayya) bai biya ni duka ba. Sai ya haɗa ni da wani Lauyansa a nan Kano muka yi magana, na yi wa lauyan bayanin ragowar kudin kayana da bai biya ni ba, sai lauyan ya ce na bar wannan zancen tun da lokacin da ya biya ban yi magana a kai ba, sai na ce to babu damuwa na bar zancen. Sai na ce to nawa za a biya ni kuɗin ƙarin kwana biyun aikin da na yi? Sai na ce ₦150,000, sai Lauyan ya ce; ya yi yawa, za a ba ki ₦100,000 sai ki mayar da ₦100,000. Na ce to babu damuwa, daga nan na tura wa Lauyan kudin ₦100,000. Wannan shi ne abin da ya faru.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adama KamayeBadakalar kudadeDiamond ZahraFimFurodusaLafiyaNasarawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Next Post

Me Ya Sa Sin Ta Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa Yayin Gasar Wasannin Olympics Ta Paris

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

19 hours ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 week ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Me Ya Sa Sin Ta Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa Yayin Gasar Wasannin Olympics Ta Paris

Me Ya Sa Sin Ta Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa Yayin Gasar Wasannin Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.