• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yadda Aka Yi Garkuwa Da Ni, Bayan Musanya Min Jariri A Asibiti’

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
garkuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adediji Moses, mahaifin ‘ya’ya uku da ya koka a shafukan sada zumunta kan zargin musanya yaron da aka haifa masa a asibitin koyarwa na Jami’ar Ladoke Akintola da ke Ogbomosho a Jihar Oyo, ya yi zargin cewa wasu mutum biyu sun yi garkuwa da shi bayan aika-aikar da aka masa.

Haka nan ya ce masu garkuwar sun yi masa barazanar cewa idan har bai janye karar da yake yi kan asibitin ba wani mugun abu zai iya faruwa da shi.

  • Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda
  • Kamfani Ya Yaye Masu Kirkirar Fasaha 1,000 A 2023

Matashin mai shekaru 34 ya zargi asibitin koyarwa na LAUTECH da laifin musanya dansa lokacin haihuwa a watan Nuwamba 2018.

Adedeji a wata hira ta musamman da ya yi da jaridar The PUNCH ya koka kan barazanar da ake yi masa tun bayan da ya fito da labarin fili.

“Kwanan nan, na ziyarci wani gidan rediyo da ke Ibadan, Agidigbo FM, inda na kuma yi bayanin halin da nake ciki. Don haka, da safe na fitar da babur dina zan fara aiki sai na ga ga wasu mutum biyu kusa da gidana amma ba su yi kama da wadanda za su hau babur ba. Da na tashi daga aiki na dawo gida da yamma. Bayan na zauna a gida na dan wani lokaci, na so in je in ga wani, a lokacin da na dawo, sai na ga mutum biyu a gefen babur dina; akwai wata mota kirar Toyota Camry kofarta a bude a can gefe.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Na ce da su don Allah su gyara ina so in dauki babur dina amma maimakon haka, sai suka tunkaro ni kamar suna son magana da ni da zuwa kusa da ni sai sika nuna min bindiga a gefena suka ce in shiga cikin motar. Na shiga mota sai suka sa wani kyalle suka rufe min fuska, don haka ban san inda aka kai ni ba. Sun yi tafiyar kusan mintuna 20 zuwa 30 kafin su tsaya. Daya daga cikinsu ya sauko ya yi waya suka fada min abubuwa da yawa.

“Suka ce aim un gaya maka idan baka dakatar da fallasa abin da ya faru da ‘yarka a sibitin LAUTECH ba to lamarin zai shafi mutane da yawa wadanda basu ji ba basu gani ba. daga nan na fara rokonsu ina gaya musu cewa ba zan jawo wa kowa wani abu ya same shi ba amma ina son ’yata da matata su yi rayuwa mai kyau kuma a kula da su sosai. Sun sake yin magana da wani ta hanyar kiran a waya a karshe sun yanke shawarar za su sake ni. Sun gargade ni cewa suna kallona kuma idan na sake daukar wani mataki za mu gauraya da su. Bayan kamar misalin karfe 10 na dare, sai suka sake daukata suka mayar da ni Orita Nira inda suka dauke ni,” in ji Adedeji.

Ya kara da cewa, “Ni da matata ba mu da aikin yi kuma ina tukin Okada ne kawai don tsira. Idan sun taimake ni, zan iya kula da iyali ba tare da damuwa game da kula da lafiyar diyata ba. Iyayena sun bani kulawa kuma haka na tsira. Na yi imanin cewa ita ma za a iya kula da ita,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Garkuwalautech
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

Next Post

Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
garkuwa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.