ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yadda Aka Yi Garkuwa Da Ni, Bayan Musanya Min Jariri A Asibiti’

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
garkuwa

Adediji Moses, mahaifin ‘ya’ya uku da ya koka a shafukan sada zumunta kan zargin musanya yaron da aka haifa masa a asibitin koyarwa na Jami’ar Ladoke Akintola da ke Ogbomosho a Jihar Oyo, ya yi zargin cewa wasu mutum biyu sun yi garkuwa da shi bayan aika-aikar da aka masa.

Haka nan ya ce masu garkuwar sun yi masa barazanar cewa idan har bai janye karar da yake yi kan asibitin ba wani mugun abu zai iya faruwa da shi.

  • Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda
  • Kamfani Ya Yaye Masu Kirkirar Fasaha 1,000 A 2023

Matashin mai shekaru 34 ya zargi asibitin koyarwa na LAUTECH da laifin musanya dansa lokacin haihuwa a watan Nuwamba 2018.

ADVERTISEMENT

Adedeji a wata hira ta musamman da ya yi da jaridar The PUNCH ya koka kan barazanar da ake yi masa tun bayan da ya fito da labarin fili.

“Kwanan nan, na ziyarci wani gidan rediyo da ke Ibadan, Agidigbo FM, inda na kuma yi bayanin halin da nake ciki. Don haka, da safe na fitar da babur dina zan fara aiki sai na ga ga wasu mutum biyu kusa da gidana amma ba su yi kama da wadanda za su hau babur ba. Da na tashi daga aiki na dawo gida da yamma. Bayan na zauna a gida na dan wani lokaci, na so in je in ga wani, a lokacin da na dawo, sai na ga mutum biyu a gefen babur dina; akwai wata mota kirar Toyota Camry kofarta a bude a can gefe.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

“Na ce da su don Allah su gyara ina so in dauki babur dina amma maimakon haka, sai suka tunkaro ni kamar suna son magana da ni da zuwa kusa da ni sai sika nuna min bindiga a gefena suka ce in shiga cikin motar. Na shiga mota sai suka sa wani kyalle suka rufe min fuska, don haka ban san inda aka kai ni ba. Sun yi tafiyar kusan mintuna 20 zuwa 30 kafin su tsaya. Daya daga cikinsu ya sauko ya yi waya suka fada min abubuwa da yawa.

“Suka ce aim un gaya maka idan baka dakatar da fallasa abin da ya faru da ‘yarka a sibitin LAUTECH ba to lamarin zai shafi mutane da yawa wadanda basu ji ba basu gani ba. daga nan na fara rokonsu ina gaya musu cewa ba zan jawo wa kowa wani abu ya same shi ba amma ina son ’yata da matata su yi rayuwa mai kyau kuma a kula da su sosai. Sun sake yin magana da wani ta hanyar kiran a waya a karshe sun yanke shawarar za su sake ni. Sun gargade ni cewa suna kallona kuma idan na sake daukar wani mataki za mu gauraya da su. Bayan kamar misalin karfe 10 na dare, sai suka sake daukata suka mayar da ni Orita Nira inda suka dauke ni,” in ji Adedeji.

Ya kara da cewa, “Ni da matata ba mu da aikin yi kuma ina tukin Okada ne kawai don tsira. Idan sun taimake ni, zan iya kula da iyali ba tare da damuwa game da kula da lafiyar diyata ba. Iyayena sun bani kulawa kuma haka na tsira. Na yi imanin cewa ita ma za a iya kula da ita,” in ji shi.

garkuwa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.