• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yadda Aka Yi Garkuwa Da Ni, Bayan Musanya Min Jariri A Asibiti’

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
garkuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adediji Moses, mahaifin ‘ya’ya uku da ya koka a shafukan sada zumunta kan zargin musanya yaron da aka haifa masa a asibitin koyarwa na Jami’ar Ladoke Akintola da ke Ogbomosho a Jihar Oyo, ya yi zargin cewa wasu mutum biyu sun yi garkuwa da shi bayan aika-aikar da aka masa.

Haka nan ya ce masu garkuwar sun yi masa barazanar cewa idan har bai janye karar da yake yi kan asibitin ba wani mugun abu zai iya faruwa da shi.

  • Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda
  • Kamfani Ya Yaye Masu Kirkirar Fasaha 1,000 A 2023

Matashin mai shekaru 34 ya zargi asibitin koyarwa na LAUTECH da laifin musanya dansa lokacin haihuwa a watan Nuwamba 2018.

Adedeji a wata hira ta musamman da ya yi da jaridar The PUNCH ya koka kan barazanar da ake yi masa tun bayan da ya fito da labarin fili.

“Kwanan nan, na ziyarci wani gidan rediyo da ke Ibadan, Agidigbo FM, inda na kuma yi bayanin halin da nake ciki. Don haka, da safe na fitar da babur dina zan fara aiki sai na ga ga wasu mutum biyu kusa da gidana amma ba su yi kama da wadanda za su hau babur ba. Da na tashi daga aiki na dawo gida da yamma. Bayan na zauna a gida na dan wani lokaci, na so in je in ga wani, a lokacin da na dawo, sai na ga mutum biyu a gefen babur dina; akwai wata mota kirar Toyota Camry kofarta a bude a can gefe.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

“Na ce da su don Allah su gyara ina so in dauki babur dina amma maimakon haka, sai suka tunkaro ni kamar suna son magana da ni da zuwa kusa da ni sai sika nuna min bindiga a gefena suka ce in shiga cikin motar. Na shiga mota sai suka sa wani kyalle suka rufe min fuska, don haka ban san inda aka kai ni ba. Sun yi tafiyar kusan mintuna 20 zuwa 30 kafin su tsaya. Daya daga cikinsu ya sauko ya yi waya suka fada min abubuwa da yawa.

“Suka ce aim un gaya maka idan baka dakatar da fallasa abin da ya faru da ‘yarka a sibitin LAUTECH ba to lamarin zai shafi mutane da yawa wadanda basu ji ba basu gani ba. daga nan na fara rokonsu ina gaya musu cewa ba zan jawo wa kowa wani abu ya same shi ba amma ina son ’yata da matata su yi rayuwa mai kyau kuma a kula da su sosai. Sun sake yin magana da wani ta hanyar kiran a waya a karshe sun yanke shawarar za su sake ni. Sun gargade ni cewa suna kallona kuma idan na sake daukar wani mataki za mu gauraya da su. Bayan kamar misalin karfe 10 na dare, sai suka sake daukata suka mayar da ni Orita Nira inda suka dauke ni,” in ji Adedeji.

Ya kara da cewa, “Ni da matata ba mu da aikin yi kuma ina tukin Okada ne kawai don tsira. Idan sun taimake ni, zan iya kula da iyali ba tare da damuwa game da kula da lafiyar diyata ba. Iyayena sun bani kulawa kuma haka na tsira. Na yi imanin cewa ita ma za a iya kula da ita,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Garkuwalautech
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Manyan Nasarori Da Kalubalen Fannin Noma A 2023”

Next Post

Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

11 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

11 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

13 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

14 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

15 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

16 hours ago
Next Post
Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

Morocco Ta Kwace Tan 1.4 Na Hodar Iblis Da Aka Boye A Cikin Ayaba

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.