• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Ittikafi Da Kuma Hukunce-Hukuncensa

by SP. Imam Ahmad Kutubi
2 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Manzon Allah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafin mu zo kan batun Ittikafi, za mu karasa bayani a kan karya azumi da muka dauko yi a makon da ya gabata a shafi na 24.
Idan mutum ya san cewa bayan kowane kwana uku ga misali zai yi rashin lafiya, ko kuwa mace ta saba da haila ta zo mata ranar bakwai ga ko wanne wata, to, da ranakunnan suka zo sai suka ki daukar azumi suna jiran faruwar wadannan uzurai.

Za su yi ramuwa game da kaffara ko da kuwa rashin lafiyan ko hailar sun auku. Yadda shari’a ta ce su yi shi ne su dauki azumin, a locin da dalilin karya shi ya zo, suka gan shi zahiri sai su karya.

  • Tafiya Ta Kama Ni A Tsakiyar Yini, Ko Zan Iya Karya Azumina?

Makaruhi ne mutum ya dandani abinci dan ya ji ko maggi ko gishiri ya yi sosai a cikin abinci ko miya. Idan ya yi sauri ya tufar azumi bai baci ba. Idan kuwa ya hadiye azumi ya baci zai yi ramuwa da kaffara.

Haka kuma makaruhi ne mutum ya tattauna abinci a cikin baki saboda kananan yara, idan ya zubar da tukan ko kufan gishirin nan ko na abincin nan azumi bai baci ba. Idan kuwa ya hadiye shi da mantuwa ko bisa ga rinjaye zai rama daya, idan kuwa da gangan ne zai yi ramuwa game da kaffara. Haka kuma wanda ya lika magani a cikin kogon hakorinsa idan bai hadiye maganin ba azumi bai karye ba.

Idan mutum mai janaba ko mace mai haila da daddare ba su samu damar yin wanka ba sai da rana, azumi yana nan. Haka kuma idan mutum ya aikata sabon Allah da daddare, komai girman zunubin nan, wajibi ne washegari ya tashi da azumi, domin zunubin sabo daban ladar yin azumi kuma daban.
Sunnah ne mutum ya kame bakinsa daga dukkanin maganganun alfasha a cikin watan Ramadana kuma ana so ya yawaita ibada ga Ubangiji Allah. Kamar yin sallar asham da karatun alkur’ani da zikiri da tasbihi da zuwa wajen tafsiri.

Labarai Masu Nasaba

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

Dukkan azumin da mutum ya karya da mantuwa ko bisa ga rinjaye, to, ba zai kara cin komai da gangan ba har rana ta fadi don alfarmar watan Ramadan, ko da yake zai rama azumin nan.

Idan kuma ya sake cin wani abu da gangan, bayan wannan na mantuwa to zai yi ramuwa game da kaffara.

Sunnah ne mai azumi ya gaggauta yin bude baki bayan ya tabbata lalle rana ta fadi. An so ya yi bude baki tun gabanin yin sallar magariba. Kuma sunnah ne ga mai yin azumi ya jinkirta sahur gwargwadon lokacin da zai isa ya karanci ayar Alkur’ani hamsin bayan kammala yin sahur kafin alfijir ya fito.

Sunnah ne ga mutum wanda ba mai hajji ba ya yi azumi ranar tara ga zulhajji, haka kuma mustahabbi ne mutum ya yi azumi cikin kwana tara na farko ga watan zulhajji.

Sunnah ne kuma ya yi azumi a rana na tara da ran goma ga muharram, da sauran kwanakin muharram, da watan rajab dana sha’aban, da kwana uku a cikin kowane wata, da kwana shida a cikin shawwal. Ana kiran wadannan da azumin Tadawwu’i, wato na sa kai.

Sunnah ne mutum ya gaggauta ramuwar azumin ramadana da ya sha. Amma Ya hallata a gare shi ya jinkirta ramuwa amma kuma dole zai rama kafin wani azumin watan ramadana ya zo. Idan kuma jinkirinsa ya yi muni har ya tsallake ramadana na gaba to zai yi sadaka da mudu daya a kowane maraice da ya rama dayan azuminsa.

Bayani A Kan Ittikafi
Ittikafi shi ne musulmi ya zauna a cikin masallaci domin yin zikiri da tasbihi da sallah da karatun Alkur’ani, yana mai yin azumi, mai kamewa daga yin jima’i da magabatan jima’i, har kwana daya ko abin da ya fi haka da niyyar yin ittikafi.

Hukuncin ittikafi sunnah ne mai lada da yawa, wajibi ne ittikafi ya zamo a cikin masallaci, mai yin sa kuma ya zamo yana mai yin azumi ko da farilla ko na tadawwi’i, kuma da sharadin kwanakin yin sa su jeru ba a yanke ba. A kallan kwanakin ittikafi kwana daya, mafi yawansa kuma kwana goma, a wani kauli kuwa an ce a kallansa kwana goma mafi yawansa wata daya.

Idan mutum zai fara kwanakin ittikafi da ya dauki alkawarin yi, zai shiga masallaci gabannin faduwar rana. Idan kuma ya kammala zai bar masallaci zuwa gida bayan magariba. Wajibi ne mutum ya cika adadin kwanakin da ya dauki alkawarin yi. Bai halatta ya rage su ba ta kowanne hali.

Mai ittikafi ba wai ba zai fita wajen masallaci ba sai domin larurar Dan’adam. Kamar tafiya cin abinci, da zuwa fitsari ko bayan gida ko wanka ko alwala. Kuma idan ya fita domin dayan wadannan abubuwa ba zai shige wuri mafi kusa da inda zai iya biyan bukatarsa ba. Idan ya je wuri mafi nisa ittikafi ya baci, sai ya faro tun daga farko. Amma idan rashin lafiya ya kama mutum, ko kuma jinin haila ko na biki ya zo wa mace, lokacin da suke yin ittikafi, to, za su fita su koma gida domin dayan wadannan uzurori. Amma da gushewar uzurinsu sai su dawo masallaci maza-maza su cigaba da ittikafinsu. Wato za su yi lissafi da kwanakin baya.

Kuma a lokacin zamansu a gida da uzuri, duk suna cikin hakkin ittikafi na barin yin jima’i da makamantansu.

Idan mai ittikafi ya ci abinci da rana da gangan ko ya yi jima’i da rana ko da daddare da gangan ko da mantuwa ittikafi ya baci, sai ya faro shi tun daga farko.

Mai ittikafi ba zai fita masallaci don gaida marasa lafiya ba, sai idan dayan iyayensa ne. Kuma ba zai fita don sallah a kan mamaci ba, ko don yin ciniki ba.

Idan karshen kwanakin ittikafin mutum ya dace da daren sallah, to, ana so ya dakata har zuwa washegari, daga nan masallaci ya zarce zuwa masallacin idi, sannan daga nan ya taho gida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah Ya Yi Wa Mai Dakin Aminu Dantata, Hajiya Rabi Rasuwa

Next Post

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

Related

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

1 week ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

2 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

3 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

1 month ago
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Dausayin Musulunci

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

2 months ago
Next Post
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

'Yan Ta'adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.