ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Ittikafi Da Kuma Hukunce-Hukuncensa

by SP. Imam Ahmad Kutubi
3 years ago
Manzon Allah

Kafin mu zo kan batun Ittikafi, za mu karasa bayani a kan karya azumi da muka dauko yi a makon da ya gabata a shafi na 24.
Idan mutum ya san cewa bayan kowane kwana uku ga misali zai yi rashin lafiya, ko kuwa mace ta saba da haila ta zo mata ranar bakwai ga ko wanne wata, to, da ranakunnan suka zo sai suka ki daukar azumi suna jiran faruwar wadannan uzurai.

Za su yi ramuwa game da kaffara ko da kuwa rashin lafiyan ko hailar sun auku. Yadda shari’a ta ce su yi shi ne su dauki azumin, a locin da dalilin karya shi ya zo, suka gan shi zahiri sai su karya.

  • Tafiya Ta Kama Ni A Tsakiyar Yini, Ko Zan Iya Karya Azumina?

Makaruhi ne mutum ya dandani abinci dan ya ji ko maggi ko gishiri ya yi sosai a cikin abinci ko miya. Idan ya yi sauri ya tufar azumi bai baci ba. Idan kuwa ya hadiye azumi ya baci zai yi ramuwa da kaffara.

ADVERTISEMENT

Haka kuma makaruhi ne mutum ya tattauna abinci a cikin baki saboda kananan yara, idan ya zubar da tukan ko kufan gishirin nan ko na abincin nan azumi bai baci ba. Idan kuwa ya hadiye shi da mantuwa ko bisa ga rinjaye zai rama daya, idan kuwa da gangan ne zai yi ramuwa game da kaffara. Haka kuma wanda ya lika magani a cikin kogon hakorinsa idan bai hadiye maganin ba azumi bai karye ba.

Idan mutum mai janaba ko mace mai haila da daddare ba su samu damar yin wanka ba sai da rana, azumi yana nan. Haka kuma idan mutum ya aikata sabon Allah da daddare, komai girman zunubin nan, wajibi ne washegari ya tashi da azumi, domin zunubin sabo daban ladar yin azumi kuma daban.
Sunnah ne mutum ya kame bakinsa daga dukkanin maganganun alfasha a cikin watan Ramadana kuma ana so ya yawaita ibada ga Ubangiji Allah. Kamar yin sallar asham da karatun alkur’ani da zikiri da tasbihi da zuwa wajen tafsiri.

LABARAI MASU NASABA

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani

Dukkan azumin da mutum ya karya da mantuwa ko bisa ga rinjaye, to, ba zai kara cin komai da gangan ba har rana ta fadi don alfarmar watan Ramadan, ko da yake zai rama azumin nan.

Idan kuma ya sake cin wani abu da gangan, bayan wannan na mantuwa to zai yi ramuwa game da kaffara.

Sunnah ne mai azumi ya gaggauta yin bude baki bayan ya tabbata lalle rana ta fadi. An so ya yi bude baki tun gabanin yin sallar magariba. Kuma sunnah ne ga mai yin azumi ya jinkirta sahur gwargwadon lokacin da zai isa ya karanci ayar Alkur’ani hamsin bayan kammala yin sahur kafin alfijir ya fito.

Sunnah ne ga mutum wanda ba mai hajji ba ya yi azumi ranar tara ga zulhajji, haka kuma mustahabbi ne mutum ya yi azumi cikin kwana tara na farko ga watan zulhajji.

Sunnah ne kuma ya yi azumi a rana na tara da ran goma ga muharram, da sauran kwanakin muharram, da watan rajab dana sha’aban, da kwana uku a cikin kowane wata, da kwana shida a cikin shawwal. Ana kiran wadannan da azumin Tadawwu’i, wato na sa kai.

Sunnah ne mutum ya gaggauta ramuwar azumin ramadana da ya sha. Amma Ya hallata a gare shi ya jinkirta ramuwa amma kuma dole zai rama kafin wani azumin watan ramadana ya zo. Idan kuma jinkirinsa ya yi muni har ya tsallake ramadana na gaba to zai yi sadaka da mudu daya a kowane maraice da ya rama dayan azuminsa.

Bayani A Kan Ittikafi
Ittikafi shi ne musulmi ya zauna a cikin masallaci domin yin zikiri da tasbihi da sallah da karatun Alkur’ani, yana mai yin azumi, mai kamewa daga yin jima’i da magabatan jima’i, har kwana daya ko abin da ya fi haka da niyyar yin ittikafi.

Hukuncin ittikafi sunnah ne mai lada da yawa, wajibi ne ittikafi ya zamo a cikin masallaci, mai yin sa kuma ya zamo yana mai yin azumi ko da farilla ko na tadawwi’i, kuma da sharadin kwanakin yin sa su jeru ba a yanke ba. A kallan kwanakin ittikafi kwana daya, mafi yawansa kuma kwana goma, a wani kauli kuwa an ce a kallansa kwana goma mafi yawansa wata daya.

Idan mutum zai fara kwanakin ittikafi da ya dauki alkawarin yi, zai shiga masallaci gabannin faduwar rana. Idan kuma ya kammala zai bar masallaci zuwa gida bayan magariba. Wajibi ne mutum ya cika adadin kwanakin da ya dauki alkawarin yi. Bai halatta ya rage su ba ta kowanne hali.

Mai ittikafi ba wai ba zai fita wajen masallaci ba sai domin larurar Dan’adam. Kamar tafiya cin abinci, da zuwa fitsari ko bayan gida ko wanka ko alwala. Kuma idan ya fita domin dayan wadannan abubuwa ba zai shige wuri mafi kusa da inda zai iya biyan bukatarsa ba. Idan ya je wuri mafi nisa ittikafi ya baci, sai ya faro tun daga farko. Amma idan rashin lafiya ya kama mutum, ko kuma jinin haila ko na biki ya zo wa mace, lokacin da suke yin ittikafi, to, za su fita su koma gida domin dayan wadannan uzurori. Amma da gushewar uzurinsu sai su dawo masallaci maza-maza su cigaba da ittikafinsu. Wato za su yi lissafi da kwanakin baya.

Kuma a lokacin zamansu a gida da uzuri, duk suna cikin hakkin ittikafi na barin yin jima’i da makamantansu.

Idan mai ittikafi ya ci abinci da rana da gangan ko ya yi jima’i da rana ko da daddare da gangan ko da mantuwa ittikafi ya baci, sai ya faro shi tun daga farko.

Mai ittikafi ba zai fita masallaci don gaida marasa lafiya ba, sai idan dayan iyayensa ne. Kuma ba zai fita don sallah a kan mamaci ba, ko don yin ciniki ba.

Idan karshen kwanakin ittikafin mutum ya dace da daren sallah, to, ana so ya dakata har zuwa washegari, daga nan masallaci ya zarce zuwa masallacin idi, sannan daga nan ya taho gida.

Ittikafi
SP. Imam Ahmad Kutubi
+ postsBio
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Karya Azumi Da Hukunce-hukuncensa
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

MASU ALAKA

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)
Dausayin Musulunci

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

September 4, 2026
Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani
Dausayin Musulunci

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani

August 28, 2026
Ittikafi
Dausayin Musulunci

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

August 21, 2026
Next Post
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

'Yan Ta'adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.