Me ake nufi da Salatin Istika? Sallar Istika tana daya daga cikin addu’o’in Sunnah da Annabi Muhammad (SAW) yake yi a lokacin fari, ko yunwa ko lokacin zafi mai tsanani.
Sallar ta kunshi raka’a biyu kuma ana fara takbirai bakwai a raka’ar farko, sannan takbirai shida a raka’a ta biyu.
Limamin yakan karanta suratul a’ala da suratul ghasiya a kowace raka’a. bayan idar da sallah limamin sai ya yi huduba daga karshe ya yi addu’a kamar yadda sunnah ta tabbatar da haka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp