• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa 

Kwalejin Yuelu Ta Jami’ar Hunan Na Kiyaye Yada Al’adun Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Kasar Sin
0
Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwalejin Yuelu tana gefen kogin Xiangjiang, da tushen dutsen Yuelu na birnin Changsha, fadar mulkin lardin Hunan dake tsakiyar kasar Sin, tana da tarihin shekaru fiye da dubu daya da kafuwa, inda kuma ake koyar da ilmi har zuwa yanzu.

A ranar 17 ga watan Satumban shekarar 2020, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ziyarci kwalejin Yuelu dake karkashin jami’ar Hunan. Lokacin da yake ziyarar aiki a lardin Hunan, inda ya nazarci yanayin horar da kwararru, da yada al’adun kasar Sin da sauransu da ake yi a kwalejin.

  • Sin: Kasashen Sin Da Afirka Za Su Nuna Abin Misali Wajen Inganta Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Daukacin Bil-Adama

Kwalejin Yuelu, daya ce daga cikin manyan kwalejoji hudu na lokacin da na kasar Sin, tana kuma yada al’adun Huxiang, wanda ke jawo mutane da dama zuwa kwalejin don samun ilmi, da karanta littattafai, da rubuta bayanai, da ajiye littattafai da sauransu don yin kokarin yada al’adun.

A yayin da shugaba Xi Jinping ya halarci taron tattaunawa kan yada al’adun kasar Sin a birnin Beijing a ranar 2 ga watan Yuni, ya jaddada cewa, ya kamata a kiyaye bude kofa ga kasashen waje, da amincewa bambancin al’adu, da bin tunanin Markisanci mai halayyar musamman na kasar Sin na zamani, da yada al’adun gargajiya na kasar Sin, da sa kaimi ga amincewa al’adun kasashen waje, da kirkiro al’adun kasar Sin mai tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin a sabon zamani. Shugaba Xi ya ce, ya kamata a kiyaye al’adu na da, da yin kirkire-kirkire, don kiyaye yada al’adun kasar Sin a zamanin yanzu.

A shekarun baya baya nan, kwalejin Yuelu ta kasance wani wuri mai alamar al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya yi kokarin yada al’adun kwalejin bada ilmi na kasar Sin, da nazarin ilmi bisa halin kasar Sin, da horar da kwararru, da kiyaye al’adun kasar Sin na tsawon shekaru fiye da dubu daya.

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

Sinawa
Jami’ar Hunan

Kiyaye yada al’adu da samar da ilmi

Kwalejin Yuelu na da matsugunni a tushen dutsen Yuelu cikin bishiyoyi, wanda hakan ke jawo hankalin dalibai, da masu yawon shakatawa da dama.

Yayin da shugaba Xi Jinping yake ziyara a kwalejin ta Yuelu, ya kalli katako da aka rubuta “Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai”, wato kamar yadda Hausawa suka ce “Dinka rigarka gwargwadon kibarka”, cikin zurfin tunani sosai ya ce, ta yaya jam’iyyar kwaminis ta Sin ta samu nasara? A lokacin, mutane fiye da 10 sun gudanar da taron farko, na wakilan jam’iyyar, har zuwa yanzu da jam’iyyar ta samu irin wannan nasara. Ya kamata a fahimci hanyar raya jam’iyyar, da kuma yadda ake yada tunanin gaskiya bisa halin da ake ciki.

A shekarar 1917, shugaban jami’ar ilmin masana’antu ta Hunan, wato jami’ar Hunan ta yanzu Bin Bucheng, ya sanya katako da aka rubuta “Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai” a kofar kwalejin Yuelu, wanda ya maida kalmomin a matsayin manufar jami’ar, don sa kaimi ga daliban jami’ar da su bi gaskiya, da koyon kimiyya da fasaha, don neman gaskiya da ilmi. Daga baya, Mao Zedong, matashi a lokacin ya taba zama a kwalejin don yin karatu, wanda ya fahimci kalmomin sosai.

Shugaba Xi Jinping ya jaddada a gun taron tattaunawa kan yada al’adun kasar Sin cewa, an raya tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin bisa tushen al’adun kasar Sin mai tarihin shekaru fiye da dubu 5, da taka hanyar hada da tunanin Marx da halin da ake ciki a kasar Sin da kuma al’adun gargajiya na kasar Sin.

A shekarun baya baya nan, kwalejin Yuelu ya kasance wani muhimmin wuri dake gwada yadda ake hada tunanin Markisanci da al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya sa kaimi ga mutane da su kara fahimci tunanin.

“Yayin da masu yawon shakatawa da dama suke shiga kwalejin Yuelu, sun rika tambayar wurin ajiye katakon da aka rubuta ‘Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai’, don kallo da fahimtar tunanin jam’iyyar kwaminis ta Sin, da tarihin kwalejin mai shekaru dubu daya.” A cewar wani dan bayani kan kwalejin mai suna Liu Feng. Ya ce, an sake kyautata bayani game da kwalejin Yuelu, wanda ya kara yin bayani game da katakon da aka rubuta “Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai”.

Kwalejin Yuelu, wuri ne na bada ilmi na tunani da siyasa na jami’ar Hunan, inda dabilai suka yi karatu a kasa da katakon, malamai da dalibai su kan yi musayar ra’ayoyi sosai a yayin karatun. Shugaban kwalejin ilmin tunanin Markisanci na jami’ar Hunan Forfesa Long Bing ya bayyana cewa, shi da dalibai suna tattauna asalin kalmomin dake kan katakon, kuma daliban suna da sha’awa sosai, abin da aka tattauna ya burge su sosai.

Tun daga watan Maris na shekarar bana, tawagar yin bayani kan tunani da siyasa ta jami’ar Hunan ta riga ta yi kwas-kwas ga tawagogin nazari daga makaratun jami’a, da midil da firamare, da jami’an jam’iyyar kwaminis ta Sin, da gwamnatin lardin Hunan, da sauran lardunan kasar Sin da yawansu ya zarce dubu 100.

Kana jami’ar Hunan ta yi nazari na musamman kan alakar dake tsakanin raya jam’iyyar kwaminis ta Sin, da al’adun gargajiya na Sin, da tarihinsu, da kuma darajarsu a zamani, don sa kaimi ga canja fasahohin Sin zuwa tunanin Sin.

Sinawa

Koyi daga lokacin da don kiyaye al’adun kasar Sin

Ana iya fahimtar maganar “Yin kokarin cimma buri, da kuma maida hankali da yanayin kasa” a dandalin Hexi, da sanin maganar “Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai” da aka rubuta a kan katako, da ganin manufar “samun ilmi tare da sanin yanayin zamantakewar al’umma” dake cikin ka’idojin kwalejin Yuelu. Kowane daki ko rubuce-rubuce, ko katako a cikin kwalejin Yuelu, yana shaida tunanin mutanen lokacin da.

Yayin da shugaba Xi Jinping ya ziyarci kwalejin Yuelu, ya jaddada cewa, ya kamata Sin ta kiyaye hanyar raya kasa, da tunaninta, da tsarinta, da kuma al’adunta, a cikinsu al’adu sun zama tushe mai zurfi dake shafar kowa da kowa. Ya kamata dalibai na lokacin yanzu, su kiyaye al’adun kasar Sin yayin da ake yada su.

An kafa kwalejin Yuelu a shekarar 976 ta daular Beisong. A lokacin daular Song, akwai masana 300 a gidan ibada na Daolin, kuma akwai dalibai 1000 a kwalejin Yuelu. A lokacin daular Qing, kashi 9 cikin 10 na manyan hafsoshi, da jami’ai sun zo ne daga lardin Hunan da Hubei. A lokacin yanzu, wato jami’ar Hunan ta kiyaye bada ilmi, kana kwalejin Yuelu ta ci gaba da koyar da ilmi, da ajiye littattafai, da kuma horar da kwararru. Duk jami’ar ta cika da yanayin koyon ilmi, da tunani, da kiyaye al’adu tun daga lokacin da zuwa halin yanzu.

“A lokacin da, kwaleji shi ne wurin da masu karatu suke neman damar samun zaman rayuwa mai kyau. Har zuwa yanzu, kwalejin daya ce daga cikin abin dake wakiltar al’adun gargajiya na kasar Sin, inda ta kiyaye tushen al’adu da tunanin kasar a cikin zuciyar Sinawa”, a cewar shugaban kwalejin Yuelu Xiao Yongming. Kana ya kara da cewa, ya kamata a bi maganar shugaba Xi Jinping, da kiyaye al’adun kasar Sin da raya su.

Dutsen Yuelu ya shahara, kana kwalejin Yuelu ita ma ta yi suna sosai. Kwalejin Yuelu ta kiyaye yin kokari don sa kaimi ga yada al’adun gargajiya na kasar Sin. Masana da dama sun yi nazari kan al’adun gargajiya na kasar Sin, har ma sun gabatar da littattafai kamar su “tarihin tsarin dabi’a na kasar Sin”, da “tarihin littattafan addinin Buddha”, da “tarihin tunanin littattafan addinin Buddha”, da “tarihin kwalejojin kasar Sin”, da “nazarin ilmi da tunani na daular Song da Yuan da Ming ta kasar Sin” da sauransu. Yayin da take daukar nauyin gudanar da aikin rubuta sabon littafi na tarihin kasar Sin, jami’ar Hunan ta shiga dandalin yin kirkire-kirkire na nazarin kalmomin lokacin da, da yada al’adun kasar Sin karo na farko, don samar da gudummawa wajen yada al’adun kasar Sin, da yada shi baki daya.

“Yin imani kan al’adun kasarmu, shi ne tushe mai zurfi dake shafar kowa da kowa. Kwalejin Yuelu yana da albarkatun al’adun gargajiya na kasar Sin, ya kamata ya kara samar da gudummawa wajen kiyaye al’adun kasar Sin, da yin imani da su.” A cewar sakataren kwamitin jam’iyyar kwaminis ta Sin na kwalejin Yuelu Chen Yuxiang.

Sinawa
Kwalejin Yuelu

Kwalejin Yuelu mai tarihin shekaru dubu daya, ta kiyaye daukar nauyin dake wuyen ta, da yin kirkire-kirkire

Yayin da shugaba Xi Jinping yake zantawa da daliban jami’ar a kwalejin Yuelu, ya yi fatan daliban za su yi namijin kokarinsu na amfani da lokaci wajen yin karatu, da koyon ilmi da fasahohi, da bin ra’ayoyi game da duniya, da zaman rayuwa, da darajar rayuwa masu dacewa, da taka hanyar zaman rayuwarsu mai dacewa, don samar da gudummawa wajen farfado da al’ummar kasar Sin.

Kwalejin Yuelu ta horar da kwararru da dama, wadanda suke da burin raya kasa. Masanan ilmin koyarwa da adabi Zhang Shi, da Zhu Xi, da Wang Yangming, sun taba koyar da ilmi a kwalejin. Mashahuran mutane a tarihin Sin Tao Shu, da Wei Yuan, da Zeng Guofan, da Zuo Zongtang sun taba yin karatu a kwalejin. Kana masu juyin mulki, da ‘yantar da jama’ar kasar Sin Mao Zedong, da He Shuheng, da Cai Hesen su ma sun taba yin karatu a kwalejin.

Jami’ar Hunan ta kiyaye neman yadda ake hada al’adun gargajiya da tunanin bada ilmi na kwalejin lokacin a da, da bada ilmi na zamanin yanzu, da kuma daukar nauyin farfado da al’ummar kasar Sin a zamanin yanzu.

A kowane watan Satumba, wato watan fara karatu a shekarun baya baya nan, ana gudanar da bikin nuna girmamawa ga malamai, a dakin taro na kwalejin Yuelu, wanda ke zama kwas na farko ga sabbin daliban jami’ar. A yayin bikin, dalibai suna rusuna wa kayan sassaka mai sifar Confucius, don nuna girmamawa gare shi. Kana suna karanta ka’idojin kwalejin Yuelu don gano tunani a cikin ka’idojin. Kaza lika suna taruwa a kasan wurin katakon da aka rubuta “Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai”, suna yin karatu da tarihin jam’iyyar kwaminis ta Sin, don sa kaimi gare su wajen yin kokari tare a sabon zamani.

“Ana koyon tunani da manufofin bada ilmi daga lokacin da don horar da kwararru ga kasarmu.” A cewar mataimakin sakataren kwamitin jam’iyyar kwaminis ta Sin na jami’ar Hunan Tang Zhenming. Kana ya ce, ana yin kokari wajen neman hanyoyin canja kwalejin ta lokacin da zuwa jami’ar zamani. Alal misali, maida hankali ga kiyaye dabi’a mai kyau, da kuma samar da wadanda suke da dabi’a yayin da suke yin karatu. Kana a yada al’adun gargajiya na kasar Sin, da darajar rayuwar dan Adam ta hanyar koyon ilmin dabi’a, da kuma hade ilmi da aiki da shi.

Sinawa
Katakon da aka rubuta “Neman gaskiya daga tabbatattun dalilai”

A kwalejin Yuelu dake jami’ar Hunan, shugaba Xi Jinping ya yi bayani ga dalibai cewa, sabon zamani na yanzu, zamani ne dake samun fitattun mutane da yawa. Shekarunsu wato shekaru 20 zuwa 30, shekaru ne mafi kyau gare su. Akwai sauran shekaru 30 daga yanzu zuwa shekarar 2050, wato shekarar cika shekaru 200 da kafuwar jam’iyyar kwaminis ta Sin, don haka ya kamata matasa sun dauki nauyin dake wuyensu a wannan zamani. Kana a horar da kwararrun matasa masu kaunar kasa.

Shugaban jami’ar Hunan Duan Xianzhong ya bayyana cewa, kwalejin Yuelu ta kiyaye tunanin tushen Sinawa, masu burin raya kasa da yada al’adun kasar Sin. Dalibai matasa sun inganta tunani ta hanyar koyon al’adun gargajiya na kasar Sin. Bayan hakan, mutane masu kammala karatu a jami’ar suna gudanar da ayyukansu, da samar da gudummawarsu a zamantakwar al’umma bisa bukatun kasar da na zamani. (Zainab Zhang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar Sojin Sama Ta Yi Asarar Jiragen Yaki 17 Cikin Shekara 8

Next Post

Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

3 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

10 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

10 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

12 months ago
Zambiya
Daga Kasar Sin

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

1 year ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Next Post
Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.