• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan Majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar Kananan hukumomin Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu (Talban Musawa) ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya turo karin sojoji jihar Katsina domin magance matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Abdullahi Aliyu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake maida martani akan wata zanga-zanga da mutanen da yake wakilta suka yi dangane da sace wasu manoma wanda ya ce karin sojoji zai taimaka matuka gaya.

  • SEMA Ta Raba Kayayyakin Gini Na Miliyan N50 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Katsina

Haka kuma ya cigaba da cewa shugaban kasa da duk wani mai ruwa da tsaki akan sha’anin tsaro suna da rawar da zai taka wajan magance wannan matsala da manoma ke fuskanta a wannan lokaci mai tsada

A cewar sa matakan da ake dauka akan sha’anin tsaro a yanzu ba za su wadatar ba, saboda haka yana ganin akwai bukatar a tallafi masu karamin karfi domin farfadowa da tattalin arzikin su na yau da kullum

Haka kuma ya nuna damuwarsa akan yadda mutanen kananan hukumomin Musawa da Matazu sun gagara yin barci da idanu biyu saboda wannan matsala, balantana kuma su je gonakin su da harkokin kasuwancin su na yau da kullum..

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Ya kara da cewa matsalar tsaro ta zama wata babar barazana ga manoman kananan hukumomin Musawa da Matazu wanda ya ce kwana nan ya bada gudunmawar taki tirela biyu ga manoman amma matsalar tsaro ta hana su zuwa gonakin su

Kazalika Hon. Abdullahi Aliyu ya yi Allah wadai da sake bullar kashe-kashe da lalata duniyoyin jama’ar jihar Katsina musamman mutanen kananan hukumomin Musawa da kuma Matazu wanda ya ce hakan ba zai ba su damar cigaba da harkokin kasuwanci ba saboda ayyukan ‘yan ta’adda

A daidai wannan gaba na ke kara kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da cewa an zo gabar da ake da bukatar karin yawan jami’an tsaron da ke jihar Katsina domin su kawo karshen salwantar da rayukan al’umma da duniyoyin su.

“Ina san shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya duba wani kyakkyawan tsari akan sha’anin tsaro da zai dawo da martabar tsaron Nijeriya musamman a wannan lokaci da abubuwa suka koma baya wanda ake bukatar kawo dangantaka mai kyau tsakanin jami’an tsaro da kuma al’umma.” Inji shi

Haka kuma dan majalisar ya bayyana cewa shugaban kasa na da ikon lalubo hanyoyin daukaka darajar hukumomin tsaro ta hanyar maida hankali akan sha’anin tattalin arziki da bayar da tsari da zai kawo karshen ‘yan ta’adda da gungun barayi .

Hon. Abdullahi Aliyu ya kara da cewa yanzu haka suna yin aiki tare da dan Majalisar dattawa na shiryar Funtua da shugaban ‘yan sandan Nijeriya domin ganin an tura jami’an tsaro 600 a shiryar Funtua baki daya.

Talban na Musawa ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa wajan ganin an samu hanyar kawo karshen ta’adanci da ‘yan ta’adda da suka adabin kananan hukumomi Musawa da Matazu ganin cewa yanki da ake yin noma.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaMatsalar TsaroNejaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa 

Next Post

Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

7 hours ago
Next Post
Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.