ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Sojoji

Dan Majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar Kananan hukumomin Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu (Talban Musawa) ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya turo karin sojoji jihar Katsina domin magance matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Abdullahi Aliyu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake maida martani akan wata zanga-zanga da mutanen da yake wakilta suka yi dangane da sace wasu manoma wanda ya ce karin sojoji zai taimaka matuka gaya.

  • SEMA Ta Raba Kayayyakin Gini Na Miliyan N50 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Katsina

Haka kuma ya cigaba da cewa shugaban kasa da duk wani mai ruwa da tsaki akan sha’anin tsaro suna da rawar da zai taka wajan magance wannan matsala da manoma ke fuskanta a wannan lokaci mai tsada

ADVERTISEMENT

A cewar sa matakan da ake dauka akan sha’anin tsaro a yanzu ba za su wadatar ba, saboda haka yana ganin akwai bukatar a tallafi masu karamin karfi domin farfadowa da tattalin arzikin su na yau da kullum

Haka kuma ya nuna damuwarsa akan yadda mutanen kananan hukumomin Musawa da Matazu sun gagara yin barci da idanu biyu saboda wannan matsala, balantana kuma su je gonakin su da harkokin kasuwancin su na yau da kullum..

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Ya kara da cewa matsalar tsaro ta zama wata babar barazana ga manoman kananan hukumomin Musawa da Matazu wanda ya ce kwana nan ya bada gudunmawar taki tirela biyu ga manoman amma matsalar tsaro ta hana su zuwa gonakin su

Kazalika Hon. Abdullahi Aliyu ya yi Allah wadai da sake bullar kashe-kashe da lalata duniyoyin jama’ar jihar Katsina musamman mutanen kananan hukumomin Musawa da kuma Matazu wanda ya ce hakan ba zai ba su damar cigaba da harkokin kasuwanci ba saboda ayyukan ‘yan ta’adda

A daidai wannan gaba na ke kara kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da cewa an zo gabar da ake da bukatar karin yawan jami’an tsaron da ke jihar Katsina domin su kawo karshen salwantar da rayukan al’umma da duniyoyin su.

“Ina san shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya duba wani kyakkyawan tsari akan sha’anin tsaro da zai dawo da martabar tsaron Nijeriya musamman a wannan lokaci da abubuwa suka koma baya wanda ake bukatar kawo dangantaka mai kyau tsakanin jami’an tsaro da kuma al’umma.” Inji shi

Haka kuma dan majalisar ya bayyana cewa shugaban kasa na da ikon lalubo hanyoyin daukaka darajar hukumomin tsaro ta hanyar maida hankali akan sha’anin tattalin arziki da bayar da tsari da zai kawo karshen ‘yan ta’adda da gungun barayi .

Hon. Abdullahi Aliyu ya kara da cewa yanzu haka suna yin aiki tare da dan Majalisar dattawa na shiryar Funtua da shugaban ‘yan sandan Nijeriya domin ganin an tura jami’an tsaro 600 a shiryar Funtua baki daya.

Talban na Musawa ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa wajan ganin an samu hanyar kawo karshen ta’adanci da ‘yan ta’adda da suka adabin kananan hukumomi Musawa da Matazu ganin cewa yanki da ake yin noma.

 

Sojoji
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.