ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Sojoji

Dan Majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar Kananan hukumomin Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu (Talban Musawa) ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya turo karin sojoji jihar Katsina domin magance matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Abdullahi Aliyu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake maida martani akan wata zanga-zanga da mutanen da yake wakilta suka yi dangane da sace wasu manoma wanda ya ce karin sojoji zai taimaka matuka gaya.

  • SEMA Ta Raba Kayayyakin Gini Na Miliyan N50 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Katsina

Haka kuma ya cigaba da cewa shugaban kasa da duk wani mai ruwa da tsaki akan sha’anin tsaro suna da rawar da zai taka wajan magance wannan matsala da manoma ke fuskanta a wannan lokaci mai tsada

ADVERTISEMENT

A cewar sa matakan da ake dauka akan sha’anin tsaro a yanzu ba za su wadatar ba, saboda haka yana ganin akwai bukatar a tallafi masu karamin karfi domin farfadowa da tattalin arzikin su na yau da kullum

Haka kuma ya nuna damuwarsa akan yadda mutanen kananan hukumomin Musawa da Matazu sun gagara yin barci da idanu biyu saboda wannan matsala, balantana kuma su je gonakin su da harkokin kasuwancin su na yau da kullum..

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya kara da cewa matsalar tsaro ta zama wata babar barazana ga manoman kananan hukumomin Musawa da Matazu wanda ya ce kwana nan ya bada gudunmawar taki tirela biyu ga manoman amma matsalar tsaro ta hana su zuwa gonakin su

Kazalika Hon. Abdullahi Aliyu ya yi Allah wadai da sake bullar kashe-kashe da lalata duniyoyin jama’ar jihar Katsina musamman mutanen kananan hukumomin Musawa da kuma Matazu wanda ya ce hakan ba zai ba su damar cigaba da harkokin kasuwanci ba saboda ayyukan ‘yan ta’adda

A daidai wannan gaba na ke kara kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da cewa an zo gabar da ake da bukatar karin yawan jami’an tsaron da ke jihar Katsina domin su kawo karshen salwantar da rayukan al’umma da duniyoyin su.

“Ina san shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya duba wani kyakkyawan tsari akan sha’anin tsaro da zai dawo da martabar tsaron Nijeriya musamman a wannan lokaci da abubuwa suka koma baya wanda ake bukatar kawo dangantaka mai kyau tsakanin jami’an tsaro da kuma al’umma.” Inji shi

Haka kuma dan majalisar ya bayyana cewa shugaban kasa na da ikon lalubo hanyoyin daukaka darajar hukumomin tsaro ta hanyar maida hankali akan sha’anin tattalin arziki da bayar da tsari da zai kawo karshen ‘yan ta’adda da gungun barayi .

Hon. Abdullahi Aliyu ya kara da cewa yanzu haka suna yin aiki tare da dan Majalisar dattawa na shiryar Funtua da shugaban ‘yan sandan Nijeriya domin ganin an tura jami’an tsaro 600 a shiryar Funtua baki daya.

Talban na Musawa ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa wajan ganin an samu hanyar kawo karshen ta’adanci da ‘yan ta’adda da suka adabin kananan hukumomi Musawa da Matazu ganin cewa yanki da ake yin noma.

 

Sojoji
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.