• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

by Bello Hamza
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Daga dukkan alamu manyan arewa daga bangarorin rayuwa daban-daban, tun daga ‘yan siyasa jami’an tsaro, tsofaffin shugabanni, sarakuna da sauran masu fada a ji a yankin arewacin Nijeriya sun tabbatar da bukatar hada kai don yi wa lamarin matsalar tsaro da ta addabi sassan arewacin kasar nan taron dangi, ‘A Yi ta ta Kare’.

Wannan kudurin ya fito fili a taron da gamayyar kungiyoyin yankin rewacin ‘Coalition Of Northern Groups’(CNG) ta gabatar a Abuja ranar Labara 24 ga watan Janairu 2024.

  • AFCON 2023: An Fitar Da Jadawalin Zagaye Na 16
  • An Maido Da Huldar Diplomasyiya Tsakanin Sin Da Nauru, CMG Ta Bude Ofishinta A Nauru

A jawabinsa, shugaban taron kuma tsohon shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar ya bayyana cewa, in har ana saon cin galabar matsalar tsaron da ke addabar yankin arewa dole a fuskanci lamarin ta haryar taron dangi tare da amfani da dabaru da dama da suka hada da karfafa jami’an tsaronmu da inganta hanyoyoyin tattara bayanan sirri tsakanin jami’anm tsaro. Haka kuma zuba jari don bukasa bangaren ilimi da tattalin arziki tare da tsunduma sarakuna cikin tafiyar da kasa zai yi mana maganin matsalar tsaro daga tushe.

Ya kuma nemi a tabbatar da hadin kai a tsakanin rundunonin tsaro don su yi aiki tare, “Dole gwamanatocin jihoji da na tarayya su hada kai a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da masu garkwua da mutane, hadin kan su tare da tafiya tare shi ne zai tabbatar da nasarar da ake bukata a wannan tafiyar’’ in ji shi.

A nasa jawabin tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya dora laifin matsalar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu a sassan Nijeriya a kan yadda aka siyasantar da lamarin tsaro, “Dole mu fuskanci harkar tsaro ba tare da la’akari siyasa ba in har muna son tabbatar da kare rayuwa da dukiyoyin al’ummar Nijeriya a wannna lokacin’’, in ji shi.

Ya kuma bukaci a yi amfani da dabaru da dama wajen yaki da ta’addanci, “Ka da mu bayar da muhimmanci kawai ga amfani da karfi a yaki da muke yi da matsalar tsaro, ya kamata a yi amfani da dabarun rungumar ‘yan ta’addan da samar musu wasu bababen more rayuwa, domin yaki kawai ba zai kai mu ga samun tabbataccen zaman lafiya ba a Nijeriya.

Haka kuma taron ya samu halatar mai alfarma Sarkin Musulmi, Abubakar Sa’ad, inda a jawabinsa ya bayyana cewa, Sarakuna a fadin tarayyar Nijeriya a shirye suke don tafiya tare da dukkan wani yunkuri  na samar da zaman lafiya a sassan Nijeriya musamman arewacin Nijeriya. Ya yi alkawarin mika sakamakon matsayar da aka cimma a taron ga taron kungiyar sarakuna arewa da za a yi a watan Faibrairu don a tattauna tare da daukar matakin da ya kamata.

Ya ce, Sarakuna na da gudummawar da za su bayar kuma za su ci gaba da bayarwa wajen tabbatar da tsaron al’umma a arewa. Ya kuma yaba wa gamayyar kungiyoyin arewa a kan shiryan taron.

A nata tsokacin, Kungiyar Dattawan Arewa, a karkashin shugabancin Farfeasa Ango Abdullahi, ta nuna jin dadinta tare da yaba wa gamayyar kungiyoyin yankin arewa da suka samu shirya wannan taron da ya zama irinsa na farko a tarihin yankin arewa.

Jawabin haka ya fito ne daga bakin mai magana da yawun kungiyar, Kwamrade Abdul-Azees Suleiman, wanda ya ce, taron da ya hada masana daga bangarori da dama zai samar da mafita da mahukunta za su yi amfani da ita wajen samar wa yankin arewa maganin matsalar tsaron da ake fuskanta wanda ta haifar da nakasu ga tattalin arzikin kasa ya kuma ci rayukan al’umma da dama a ‘yan skekarun nan.

Ya kuma ce, taron ya samar da dandamalin da masana za su baje kolinsu a kan yadda za a kawo karshen mastalar tsaro a kasar na, a kan haka ya bukacu hukumomin gwamnatocin jihohi da na tarayya su rungumi matsayar da taron ya fitar don yin aiki da su, ta haka za a tabbatar da nasarar da ake bukata.

Da yake jawabin godiya ga maharta taron, daya daga cikin jagororin da suka shirya taron, Dakta Nastura Ashir Shariff ya bayyana yadda matsalar tsaro ta shafi dukkan bangaren rayuwar al’ummar Nijeriya musamman yankin arewa.

Ya kuma amince da shawarar cewa, yaki da mastalar tsaro na bukatar hadin kan dukkan bangarorin al’umma da kuma aiki tare a tsakanin gwamnatin jihohi da na tarayya har zuwa matakin kananan hukumomi,. Ya nemi hadin kai da kasashe makwabta domin ta haka za a iya dakile rikice-rikicen da ke tsallakowa daga waje zuwa cikin gida Nijeriya.

Nastura Ashir Shariff ya kuma nemi gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da talauci da tsadar rayuwa da al’umma ke fuskanta, ya ce, matsalar rashin aiki yi a tsakanin matasa yana taimakawa wajen yaudarar matasanmu su fada ayyukan ta’addanci.

Daga karshe ya nemi gwammati ta yi amfani da dukkan sakamakon da taron ya fitar don kawo karshen matsalar tsaro a yankin arewa. Taron ya samu halarta gwamnoni, sarakuna gargajiya, masana harkokin tsaro da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Munakisar Dauke Sassan CBN Da FAAN Daga Abuja Zuwa Legas…

Next Post

‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

8 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

9 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

17 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

22 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

1 day ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

'Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.