• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

byBello Hamza
2 years ago
Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Dogaron ba bankuna Nijeriya ke yi wa Babban Bankin Nijeriya (CBN) a wajen gudanar da harkokinsu yana ta kara karuwa yayin da bayani ya nuna cewa, bankunan Nijeriya sun wawuri bashin fiye da Naira Tiriliyan 3.03 a watan Satumba alhali a watan Agusta bashin Naira biliyan 323.97 suka karba, wanda hakan ke nuna an samu karuwar kashi 835 na bashin da suka ci daga watan Agusta.

Haka kuma bayani ya nuna cewa, babban bankin ya zuba jarin fiye naira Tiriliyan 10  a bangarorin tattalin kasa daban-daban amma kuma babu wani abin a zo a gani, don kudaden da aka zuba basu nuna wani gaggarumin bunkasar tattalin arzikin kasar ba.

  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
  • Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

Bayanai daga shafin intanet na Babban Bankin ya nuna cewa, tun daga farkon watan Satumba har zuwa ranar Juma’a 22 ga watan basussukan kudi da bankuna kasuwancin kasar nan suka karba ya kai Naira Tiriliyan 3.028, amma a watan Agusta bankuna sun karbi bashin naira Biliyan 323.97, wannan ya sa masana ke bayanin cewa, lallai dogaron da bankuna kasuwanci ke yi wa Babban Bankin kasa ya yi yawa, kuma hakan ba zai harfar wa tattalin arzikin kaasa da mai ido ba.

Bankuna sun karbi kudaden ne ta hanyar tsarin bayar da bashi na CBN mai suna “Standing Lending Facility (SLF)” wanda tsari ne ta yadda bankuna za su iya karbar kudade don biyan bukatun su na kusa da kuma na nesa, musamman yayin da abokan huddarsu suka bukaci karbar kudi masu yawa a lokaci daya.

Amfani da tsari na SLF na nuna cewa, Banki na fuskantar tsananin bukatar kudi ko kuma yana jin jiki sakamakon tsare-tsaren Babban Banki ko kuma yana fuskanta wasu basussuka da ya kasa karbar daga abokan hulda’

A cikin shekaru biyu da suka wuce, CBN ya bullo da wasu tsare-tsare da suka tilastawa bankuna shiga matsalar rashin tsabar kudi wanda hakan ya haifar da bukatar su nemi kudi a kusan duk mako don abokan huldar su, ana kuma tunanin wannan na daga cikin dalilin da haifar da yawan bashin da bankunan suke ci.

Haka kuma wasu mambobin kwamitin kula da yadda CBN ke sarrafa kudade sun bayyana cewa, tsarin Babban Bankin yana da alfanu ga tattalin arzikin kasa kuma Baban Bankiin na a kan tsarin da gwamnati ta dora shi, sun kuma yaba da yadda bankuna ke gudanar da harkokinsu. Wani mamba a kwamitin mai suna Adenikinju Festus, ya ce, bankuna sun yi kokari amma lallai ya kamata su kara kaimi, amma lallai ya kamata a yaba musu don bayani ya nuna cewa, harkokinsu ya karu daga kashi 11.2 a watan Yuni na shekarar 2023 zuwa 13 a watan Mayu na shekarar Mayu 2023. Ya kuma nemi su bude wasu hanyoyin samun kudade su rage dogaro da babban Banki, ta haka tattalin arzikin kasar zai bunkasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version