• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

by Bello Hamza
2 years ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Dogaron ba bankuna Nijeriya ke yi wa Babban Bankin Nijeriya (CBN) a wajen gudanar da harkokinsu yana ta kara karuwa yayin da bayani ya nuna cewa, bankunan Nijeriya sun wawuri bashin fiye da Naira Tiriliyan 3.03 a watan Satumba alhali a watan Agusta bashin Naira biliyan 323.97 suka karba, wanda hakan ke nuna an samu karuwar kashi 835 na bashin da suka ci daga watan Agusta.

Haka kuma bayani ya nuna cewa, babban bankin ya zuba jarin fiye naira Tiriliyan 10  a bangarorin tattalin kasa daban-daban amma kuma babu wani abin a zo a gani, don kudaden da aka zuba basu nuna wani gaggarumin bunkasar tattalin arzikin kasar ba.

  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
  • Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

Bayanai daga shafin intanet na Babban Bankin ya nuna cewa, tun daga farkon watan Satumba har zuwa ranar Juma’a 22 ga watan basussukan kudi da bankuna kasuwancin kasar nan suka karba ya kai Naira Tiriliyan 3.028, amma a watan Agusta bankuna sun karbi bashin naira Biliyan 323.97, wannan ya sa masana ke bayanin cewa, lallai dogaron da bankuna kasuwanci ke yi wa Babban Bankin kasa ya yi yawa, kuma hakan ba zai harfar wa tattalin arzikin kaasa da mai ido ba.

Bankuna sun karbi kudaden ne ta hanyar tsarin bayar da bashi na CBN mai suna “Standing Lending Facility (SLF)” wanda tsari ne ta yadda bankuna za su iya karbar kudade don biyan bukatun su na kusa da kuma na nesa, musamman yayin da abokan huddarsu suka bukaci karbar kudi masu yawa a lokaci daya.

Amfani da tsari na SLF na nuna cewa, Banki na fuskantar tsananin bukatar kudi ko kuma yana jin jiki sakamakon tsare-tsaren Babban Banki ko kuma yana fuskanta wasu basussuka da ya kasa karbar daga abokan hulda’

A cikin shekaru biyu da suka wuce, CBN ya bullo da wasu tsare-tsare da suka tilastawa bankuna shiga matsalar rashin tsabar kudi wanda hakan ya haifar da bukatar su nemi kudi a kusan duk mako don abokan huldar su, ana kuma tunanin wannan na daga cikin dalilin da haifar da yawan bashin da bankunan suke ci.

Haka kuma wasu mambobin kwamitin kula da yadda CBN ke sarrafa kudade sun bayyana cewa, tsarin Babban Bankin yana da alfanu ga tattalin arzikin kasa kuma Baban Bankiin na a kan tsarin da gwamnati ta dora shi, sun kuma yaba da yadda bankuna ke gudanar da harkokinsu. Wani mamba a kwamitin mai suna Adenikinju Festus, ya ce, bankuna sun yi kokari amma lallai ya kamata su kara kaimi, amma lallai ya kamata a yaba musu don bayani ya nuna cewa, harkokinsu ya karu daga kashi 11.2 a watan Yuni na shekarar 2023 zuwa 13 a watan Mayu na shekarar Mayu 2023. Ya kuma nemi su bude wasu hanyoyin samun kudade su rage dogaro da babban Banki, ta haka tattalin arzikin kasar zai bunkasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kokarin Jihohi Na Cin Gajiyar Albarkatun Ma’adanai: Dobi Ga Jihar Kaduna

Next Post

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

2 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

1 week ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

3 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

3 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.