ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

by Bello Hamza
3 years ago
Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Dogaron ba bankuna Nijeriya ke yi wa Babban Bankin Nijeriya (CBN) a wajen gudanar da harkokinsu yana ta kara karuwa yayin da bayani ya nuna cewa, bankunan Nijeriya sun wawuri bashin fiye da Naira Tiriliyan 3.03 a watan Satumba alhali a watan Agusta bashin Naira biliyan 323.97 suka karba, wanda hakan ke nuna an samu karuwar kashi 835 na bashin da suka ci daga watan Agusta.

Haka kuma bayani ya nuna cewa, babban bankin ya zuba jarin fiye naira Tiriliyan 10  a bangarorin tattalin kasa daban-daban amma kuma babu wani abin a zo a gani, don kudaden da aka zuba basu nuna wani gaggarumin bunkasar tattalin arzikin kasar ba.

  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
  • Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

Bayanai daga shafin intanet na Babban Bankin ya nuna cewa, tun daga farkon watan Satumba har zuwa ranar Juma’a 22 ga watan basussukan kudi da bankuna kasuwancin kasar nan suka karba ya kai Naira Tiriliyan 3.028, amma a watan Agusta bankuna sun karbi bashin naira Biliyan 323.97, wannan ya sa masana ke bayanin cewa, lallai dogaron da bankuna kasuwanci ke yi wa Babban Bankin kasa ya yi yawa, kuma hakan ba zai harfar wa tattalin arzikin kaasa da mai ido ba.

Bankuna sun karbi kudaden ne ta hanyar tsarin bayar da bashi na CBN mai suna “Standing Lending Facility (SLF)” wanda tsari ne ta yadda bankuna za su iya karbar kudade don biyan bukatun su na kusa da kuma na nesa, musamman yayin da abokan huddarsu suka bukaci karbar kudi masu yawa a lokaci daya.

Amfani da tsari na SLF na nuna cewa, Banki na fuskantar tsananin bukatar kudi ko kuma yana jin jiki sakamakon tsare-tsaren Babban Banki ko kuma yana fuskanta wasu basussuka da ya kasa karbar daga abokan hulda’

A cikin shekaru biyu da suka wuce, CBN ya bullo da wasu tsare-tsare da suka tilastawa bankuna shiga matsalar rashin tsabar kudi wanda hakan ya haifar da bukatar su nemi kudi a kusan duk mako don abokan huldar su, ana kuma tunanin wannan na daga cikin dalilin da haifar da yawan bashin da bankunan suke ci.

Haka kuma wasu mambobin kwamitin kula da yadda CBN ke sarrafa kudade sun bayyana cewa, tsarin Babban Bankin yana da alfanu ga tattalin arzikin kasa kuma Baban Bankiin na a kan tsarin da gwamnati ta dora shi, sun kuma yaba da yadda bankuna ke gudanar da harkokinsu. Wani mamba a kwamitin mai suna Adenikinju Festus, ya ce, bankuna sun yi kokari amma lallai ya kamata su kara kaimi, amma lallai ya kamata a yaba musu don bayani ya nuna cewa, harkokinsu ya karu daga kashi 11.2 a watan Yuni na shekarar 2023 zuwa 13 a watan Mayu na shekarar Mayu 2023. Ya kuma nemi su bude wasu hanyoyin samun kudade su rage dogaro da babban Banki, ta haka tattalin arzikin kasar zai bunkasa.

Bankuna
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.