ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

by Bello Hamza
3 years ago
Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

Dogaron ba bankuna Nijeriya ke yi wa Babban Bankin Nijeriya (CBN) a wajen gudanar da harkokinsu yana ta kara karuwa yayin da bayani ya nuna cewa, bankunan Nijeriya sun wawuri bashin fiye da Naira Tiriliyan 3.03 a watan Satumba alhali a watan Agusta bashin Naira biliyan 323.97 suka karba, wanda hakan ke nuna an samu karuwar kashi 835 na bashin da suka ci daga watan Agusta.

Haka kuma bayani ya nuna cewa, babban bankin ya zuba jarin fiye naira Tiriliyan 10  a bangarorin tattalin kasa daban-daban amma kuma babu wani abin a zo a gani, don kudaden da aka zuba basu nuna wani gaggarumin bunkasar tattalin arzikin kasar ba.

  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
  • Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

Bayanai daga shafin intanet na Babban Bankin ya nuna cewa, tun daga farkon watan Satumba har zuwa ranar Juma’a 22 ga watan basussukan kudi da bankuna kasuwancin kasar nan suka karba ya kai Naira Tiriliyan 3.028, amma a watan Agusta bankuna sun karbi bashin naira Biliyan 323.97, wannan ya sa masana ke bayanin cewa, lallai dogaron da bankuna kasuwanci ke yi wa Babban Bankin kasa ya yi yawa, kuma hakan ba zai harfar wa tattalin arzikin kaasa da mai ido ba.

Bankuna sun karbi kudaden ne ta hanyar tsarin bayar da bashi na CBN mai suna “Standing Lending Facility (SLF)” wanda tsari ne ta yadda bankuna za su iya karbar kudade don biyan bukatun su na kusa da kuma na nesa, musamman yayin da abokan huddarsu suka bukaci karbar kudi masu yawa a lokaci daya.

Amfani da tsari na SLF na nuna cewa, Banki na fuskantar tsananin bukatar kudi ko kuma yana jin jiki sakamakon tsare-tsaren Babban Banki ko kuma yana fuskanta wasu basussuka da ya kasa karbar daga abokan hulda’

A cikin shekaru biyu da suka wuce, CBN ya bullo da wasu tsare-tsare da suka tilastawa bankuna shiga matsalar rashin tsabar kudi wanda hakan ya haifar da bukatar su nemi kudi a kusan duk mako don abokan huldar su, ana kuma tunanin wannan na daga cikin dalilin da haifar da yawan bashin da bankunan suke ci.

Haka kuma wasu mambobin kwamitin kula da yadda CBN ke sarrafa kudade sun bayyana cewa, tsarin Babban Bankin yana da alfanu ga tattalin arzikin kasa kuma Baban Bankiin na a kan tsarin da gwamnati ta dora shi, sun kuma yaba da yadda bankuna ke gudanar da harkokinsu. Wani mamba a kwamitin mai suna Adenikinju Festus, ya ce, bankuna sun yi kokari amma lallai ya kamata su kara kaimi, amma lallai ya kamata a yaba musu don bayani ya nuna cewa, harkokinsu ya karu daga kashi 11.2 a watan Yuni na shekarar 2023 zuwa 13 a watan Mayu na shekarar Mayu 2023. Ya kuma nemi su bude wasu hanyoyin samun kudade su rage dogaro da babban Banki, ta haka tattalin arzikin kasar zai bunkasa.

Bankuna
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Ba Da Lambar Yabo Ga Ayyukan Ba Da Ilmi Ga Yara Mata Da Mata Na UNESCO Na Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.