• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Binciken Kayan Tarihi Ke Zakulo Asalin Magabata Da Wayewar Kansu A Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Tarihi

A yadda na fahimci Sinawa, mutane ne da suka fahimci zamaninsu ta hanyar amfani da wayewar zamanin magabatansu. Kamar maganar ta zamo a dunkule ko? Abin da nake nufi shi ne, Sinawa sun fahimci muhimmancin wayewar kan magabatansu, don haka suka nace da bincike a kan kayayyakin tarihinsu tare da amfani da abubuwan da suka gano wajen zamanantar da kasarsu da kuma kara tabbatar da asalin tarihinsu.

Wasu abubuwa da aka gano na tarihi bisa amfani da ilimin kimiyyar kayan tarihi a ’yan shekarun nan a sassan kasar Sin sun kara fahimtar da Sinawa asalin tsohon tarihinsu, tare da yin amfani da kayayyakin bincike na zamani wajen gano tushen wayewarsu da ta kunshi samuwar dan’adam da kuma aikin gona.

  • Kwamishinan Tsaron Cikin Gida Na Kano Ya Yi Murabus Watanni 7 Bayan Naɗa Shi
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

Akwai wasu kokunan kawunan mutane guda uku da aka gano a birnin Shiyan na lardin Hubei da ke tsakiyar kasar Sin, wadanda bincike ya gano tabbas dan’adam ya taba rayuwa a doron kasa a yankin kasar Sin tun fiye da shekaru miliyan da suka gabata.

Babba daga cikin kokunan kawunan wadanda aka yi wa lakabi da “Dan’adam na Yunxian” da aka gano a watan Disamban 2022, ya kasance daya daga cikin sassan jikin dan’adam mafi adanawa da aka taba ganowa a daukacin yankin Turai da na Asiya. Tawagar da ta gano kokon kan a karkashin kasa ta yi amfani da ingantacciyar na’urar 3D mai tantance gaskiyar wanzuwar abu, wajen sake fasalta fuskar mai kokon kan, inda hakan ya taimaka da wasu bayanai a fannin binciken samuwar dan’adam a doron kasa da kuma yanayin ci gaban bil’adama a farko-farkon zamani.

Kazalika, gagarumar nasarar da Sinawa suka samu a wurin binciken tarihi na Shangshan da ke lardin Zhejiang a gabashin kasar Sin ta sake tabbatar da cewa, kasar Sin ce ta fara noman shinkafa a duniya. Masana kimiyyar tarihi sun gano burbushin shinkafar da aka yi imanin ta kai tsawon shekaru 10,000 a duniya, a wurin binciken. Wannan ya nuna irin rawar da magabatan Sinawa suka taka wajen aikin gona da kuma wayewar kan dan’adam a gabashin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Har ila yau, masu bincike sun gano wasu tsoffin dabarun hana koguna da madatsun ruwa ambaliya da yadda aka tsaga manyan hanyoyin ruwa da aka yi amfani da su shekaru 5,000 da suka gabata, a wani tsohon yanki na Zhejiang ta hanyar amfani da kayan binciken muhalli. Binciken ya fayyace wayewar kai na tsara birane da kula da koguna da hanyoyin ruwa irin na Liangzhu a tsohon zamani.

Babu shakka, amfani da wayewar kan magabata a zamaninmu na yanzu yana daga cikin sirrin nasarorin da Sinawa ke samu ta fuskar wayewar kai da bunkasa ci gaban kimiyya da fasaha da kere-kere da kirkire-kirkire. Ina fatan kasashenmu na Afirka su dau hannu domin jifar tsuntsu biyu da dutse daya, tabbatar da tarihinmu na asali, da amfani da wayewar kan magabata wajen samun ci gaba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Next Post
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar

Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.