• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Darajar Naira Ta Fadi Da Kashi 215 Cikin 100 A Shekara Daya

by Sani Anwar
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Darajar Naira Ta Fadi Da Kashi 215 Cikin 100 A Shekara Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan hade kasuwar hada-hadar kudaden kasashen waje da ta Nijeriya shekara guda da ta gabata, darajar Naira ta fadi da kusan kashi 214.64 cikin 100, idan aka kwatanta ta da dala.

A yayin rufe kasuwar a ranar Juma’a, Naira ta kasance a matsayin Naira 1482.72 kan duk dala guda, idan aka kwatanta da Naira 471 a kan kowace dala daya a shekarar da ta gabata.

  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya
  • Kawar da Shaye-Shayen Tamkar Kawar da Miyagun Laifuka Ne – Kwamandan NDLEA Na Kebbi

Sanarwar da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayar, na soke hada-hadar kasuwancin kudaden waje a rukuni daban-daban da ya bayyana cewa, “Yanzu dai, za a gudanar da dukkanin hada-hadar ta hanyar masu zuba hannun jari da kuma masu fitar da kayayyaki, inda harkokin saye da sayarwa na kasuwar za su tantance farashin canjin.

Sannan, za a ci gaba da gudanar harkokin da suka shafi harkar lafiya, biyan kudin makarantu, harkokin kanana da matsakaitun masana’antu da sauran makamantansu ta hanyar bankuna.”

Bankin na CBN, ya kuma sake sanar da bullo da tsarin mai son saye da kuma mai son sayarwa, wanda hakan zai ba da damar yin mu’amala da ta cancanta, domin samun musayar kudaden kasashen waje a kan ka’idojin da aka zayyana kan jadawali mai dauke da kwanan watan 21 ga watan Afrilun 2017.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Tun lokacin da kudin Nijeriya ke shawagi, ya ci gaba da kasancewa cikin jula-jula; duk kuwa da kokarin da Babban Bankin Kasa (CBN) ke yi, karkashin jagorancin Dakta Olayemi Cardoso na ganin ya daidaita shi.

A karshen shekarar 2023, Naira ta kai 911 a matsayin duk dala guda, wanda hakan ke nuna faduwarta cikin watanni shida.

A sharhin da ‘Fitch Ratings’ ta yi a watan Fabrairu, ta bayyana faduwar darajar Nairar da kusan kashi 40 cikin 100; inda ta ce, “Darajar Naira ta yi matukar faduwa a ‘yan kwanakin nan da kusan kashi 40 cikin 100, wanda ya zarce matsakaicin abin da aka yi tsammani na faduwar darajar Nairar a shekarar 2024.

Har ila yau, babbar faduwar darajar Nairar a karo na biyu a shekarar (ragin kashi 70 cikin 100 tun a shekarar 2022), wanda ya hadu da kimar musaya ta farashin gwamnati da kuma ta kasuwar bayan fage.”

A cikin sabuwar shekara, darajar Naira ta yi matukar faduwa warwas, inda ta kai kusan Naira 2000 kan duk dala daya; wanda hakan ya haifar da cece-kucen cewa, masu yin bi ta da kulle a kan ciniki ko hada-hadar dalar na samun nasara wajen yunkurin dakile darajar Nairar.

Haka zalika, kudin ya tashi daga matsayin kudin da keg an gaba a daraja a watan Mayu zuwa kudi mafi lalacewa a duniya a watan Afrilu, a cewar rahoton Bloomberg.

Duk a cikin wannan, babban bankin CBN; ya fitar da daftarin aiki tare da daukar matakan daidaita darajar Naira da kuma habaka samar da kudaden waje.

Da yake yin tsokaci a kan halin da Nairar ke ciki, shekara daya bayan aiwatar da gagarumin garambawul, masanin tattalin arziki kuma babban jami’in hulda da jama’a na tattalin arziki Ayo Teriba, ya yaba wa Babban Bankin Kasa (CBN); wanda Olayemi Cardoso ke jagoranta, kan yadda yake kokari wajen tafiyar da harkokin kasuwancin kudaden wajen a matsayin na bai-daya.

Ya kara da cewa, idan aka kwatanta batun cire tallafin man fetir, kasuwar hada-hadar kudaden waje za ta yi matukar kyau.

“Zan iya cewa, Naira ta yi matukar kyau fiye da farashin man fetir. Duk manufofi biyun ne aka yi gaggawar aiwatar das u; ba tare da aiwatar da kyakkyawan shiri ba. Amma dai, game da kasuwar canji; an yi gyare-gyaren day a kamata bayan samun sassaucin ra’ayi, sannan kuma dole ne ku yaba wa gwamnan babban bankin kasar da tawagarsa.

“An nada shi (Cardoso), watanni uku bayan aiwatar da farashi na bai-daya. Kazalika, ya yi kokari wajen warware matsalar rashin gaskiya a kasuwanni. Akwai kuma karin day a fito karara kan basussukan day a gada a lokacin, inda ya bayyana abin da za su rika biya har su kamala biya baki-daya da kuma wani kaso da aka yi sama da fadi da shi.

“Sannan, ya kuma bude kasuwa don sake fadada harkar, saboda haka, dole ne a yaba wa mulkinsa a halin yanzu; sun kuma soke ko haramta abubuwa 43, sun bai wa masu harkar canji damar ci gaba da harkokinsu tare da bai wa masu musayar kudade daban-daban na kasa da kasa lasisi aiwatar da kasuwancinsu. Za a iya bai wa kowa wannan mukami, amma baa bin mamaki ba ne idan aka ga wannan farashi ya yi tashin gwauron zabi.”

Sai dai kuma, Teriba ya nuna damuwarsa kan yadda kasuwar ke ci gaba da tabarbarewa, duk da cewa kuma ya nuna kwarin gwiwar da Babban Bankin CBN da kwamitin kula da harkokin kudi ked a shi, na iya shawo kan al’amarin.

“Abin da kawai ke damun wannan hada-hada ta canjin kudi shi ne, rashin samun daidaito, wanda Babban Bankin Kasa kuma da kwamitin kula da harkokin kudi ke kokari, don magancewa; wanda ko shakka babu a karshe za su iya magancewar. Amma hakan ba zai yiwu ba, ba tare da sake fasalin cire tallafin man fetir ba,” kamar yadda ya tabbatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DarajaFaduwaNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

Next Post

Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

3 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

3 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

4 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

4 weeks ago
Next Post
Barazanar Da Noman Masara Da Wake Ke Fuskanta A Nahiyar Afirka

Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.