• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Darajar Naira Ta Fadi Da Kashi 215 Cikin 100 A Shekara Daya

by Sani Anwar
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Yadda Darajar Naira Ta Fadi Da Kashi 215 Cikin 100 A Shekara Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan hade kasuwar hada-hadar kudaden kasashen waje da ta Nijeriya shekara guda da ta gabata, darajar Naira ta fadi da kusan kashi 214.64 cikin 100, idan aka kwatanta ta da dala.

A yayin rufe kasuwar a ranar Juma’a, Naira ta kasance a matsayin Naira 1482.72 kan duk dala guda, idan aka kwatanta da Naira 471 a kan kowace dala daya a shekarar da ta gabata.

  • Rasuwar Suruka: Gwamnoni Sun Kai Wa Shettima Ziyarar Ta’aziyya
  • Kawar da Shaye-Shayen Tamkar Kawar da Miyagun Laifuka Ne – Kwamandan NDLEA Na Kebbi

Sanarwar da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayar, na soke hada-hadar kasuwancin kudaden waje a rukuni daban-daban da ya bayyana cewa, “Yanzu dai, za a gudanar da dukkanin hada-hadar ta hanyar masu zuba hannun jari da kuma masu fitar da kayayyaki, inda harkokin saye da sayarwa na kasuwar za su tantance farashin canjin.

Sannan, za a ci gaba da gudanar harkokin da suka shafi harkar lafiya, biyan kudin makarantu, harkokin kanana da matsakaitun masana’antu da sauran makamantansu ta hanyar bankuna.”

Bankin na CBN, ya kuma sake sanar da bullo da tsarin mai son saye da kuma mai son sayarwa, wanda hakan zai ba da damar yin mu’amala da ta cancanta, domin samun musayar kudaden kasashen waje a kan ka’idojin da aka zayyana kan jadawali mai dauke da kwanan watan 21 ga watan Afrilun 2017.

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Tun lokacin da kudin Nijeriya ke shawagi, ya ci gaba da kasancewa cikin jula-jula; duk kuwa da kokarin da Babban Bankin Kasa (CBN) ke yi, karkashin jagorancin Dakta Olayemi Cardoso na ganin ya daidaita shi.

A karshen shekarar 2023, Naira ta kai 911 a matsayin duk dala guda, wanda hakan ke nuna faduwarta cikin watanni shida.

A sharhin da ‘Fitch Ratings’ ta yi a watan Fabrairu, ta bayyana faduwar darajar Nairar da kusan kashi 40 cikin 100; inda ta ce, “Darajar Naira ta yi matukar faduwa a ‘yan kwanakin nan da kusan kashi 40 cikin 100, wanda ya zarce matsakaicin abin da aka yi tsammani na faduwar darajar Nairar a shekarar 2024.

Har ila yau, babbar faduwar darajar Nairar a karo na biyu a shekarar (ragin kashi 70 cikin 100 tun a shekarar 2022), wanda ya hadu da kimar musaya ta farashin gwamnati da kuma ta kasuwar bayan fage.”

A cikin sabuwar shekara, darajar Naira ta yi matukar faduwa warwas, inda ta kai kusan Naira 2000 kan duk dala daya; wanda hakan ya haifar da cece-kucen cewa, masu yin bi ta da kulle a kan ciniki ko hada-hadar dalar na samun nasara wajen yunkurin dakile darajar Nairar.

Haka zalika, kudin ya tashi daga matsayin kudin da keg an gaba a daraja a watan Mayu zuwa kudi mafi lalacewa a duniya a watan Afrilu, a cewar rahoton Bloomberg.

Duk a cikin wannan, babban bankin CBN; ya fitar da daftarin aiki tare da daukar matakan daidaita darajar Naira da kuma habaka samar da kudaden waje.

Da yake yin tsokaci a kan halin da Nairar ke ciki, shekara daya bayan aiwatar da gagarumin garambawul, masanin tattalin arziki kuma babban jami’in hulda da jama’a na tattalin arziki Ayo Teriba, ya yaba wa Babban Bankin Kasa (CBN); wanda Olayemi Cardoso ke jagoranta, kan yadda yake kokari wajen tafiyar da harkokin kasuwancin kudaden wajen a matsayin na bai-daya.

Ya kara da cewa, idan aka kwatanta batun cire tallafin man fetir, kasuwar hada-hadar kudaden waje za ta yi matukar kyau.

“Zan iya cewa, Naira ta yi matukar kyau fiye da farashin man fetir. Duk manufofi biyun ne aka yi gaggawar aiwatar das u; ba tare da aiwatar da kyakkyawan shiri ba. Amma dai, game da kasuwar canji; an yi gyare-gyaren day a kamata bayan samun sassaucin ra’ayi, sannan kuma dole ne ku yaba wa gwamnan babban bankin kasar da tawagarsa.

“An nada shi (Cardoso), watanni uku bayan aiwatar da farashi na bai-daya. Kazalika, ya yi kokari wajen warware matsalar rashin gaskiya a kasuwanni. Akwai kuma karin day a fito karara kan basussukan day a gada a lokacin, inda ya bayyana abin da za su rika biya har su kamala biya baki-daya da kuma wani kaso da aka yi sama da fadi da shi.

“Sannan, ya kuma bude kasuwa don sake fadada harkar, saboda haka, dole ne a yaba wa mulkinsa a halin yanzu; sun kuma soke ko haramta abubuwa 43, sun bai wa masu harkar canji damar ci gaba da harkokinsu tare da bai wa masu musayar kudade daban-daban na kasa da kasa lasisi aiwatar da kasuwancinsu. Za a iya bai wa kowa wannan mukami, amma baa bin mamaki ba ne idan aka ga wannan farashi ya yi tashin gwauron zabi.”

Sai dai kuma, Teriba ya nuna damuwarsa kan yadda kasuwar ke ci gaba da tabarbarewa, duk da cewa kuma ya nuna kwarin gwiwar da Babban Bankin CBN da kwamitin kula da harkokin kudi ked a shi, na iya shawo kan al’amarin.

“Abin da kawai ke damun wannan hada-hada ta canjin kudi shi ne, rashin samun daidaito, wanda Babban Bankin Kasa kuma da kwamitin kula da harkokin kudi ke kokari, don magancewa; wanda ko shakka babu a karshe za su iya magancewar. Amma hakan ba zai yiwu ba, ba tare da sake fasalin cire tallafin man fetir ba,” kamar yadda ya tabbatar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DarajaFaduwaNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci MDD Da Ta Mai Da Hankali Ga Matsalolin Jin Kai Da Ba A Samar Musu Da Isassun Kudade

Next Post

Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

13 hours ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

1 week ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

2 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

3 weeks ago
Next Post
Barazanar Da Noman Masara Da Wake Ke Fuskanta A Nahiyar Afirka

Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.