• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gobara Ta Kone Wani Kauye Kurmus A Jigawa

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Gobara Ta Kone Wani Kauye Kurmus A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata gobara ta kone wani kauye mai suna Barebari da ke karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Shugaban karamar hukumar Shehu Sule Udi ne ya sanar da haka lokacin da yake zanta wa da manema labarai.

  • An Fitar Da Tsarin Yin Kwaskwarima Na JKS Da Hukumomin Gwamnati
  • EFCC Ta Gurfanar Da Farfesa A Gaban Kuliya Bisa Zargin Damfarar N1.4bn

Ya ce, gobarar ta tashi tashi ne da safe, ta kuma kone gidaje masu yawa da runbunan da aka adana amfanin gona da dabbobi da kuma wasu kadarori masu yawa.

Udi ya ce, an taba yin irin wannan gobarar sheka biyu da ta wuce a wannan kauyen, wadda ta yi sanadiyyar konewar rabin kauyen.

Saboda haka, sai ya yi kira ga mutanen wannan yanki da su kara lura sosai wajen yin amfani da wuta, domin guje wa afkuwar irin wannan nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Ya ce, yanzu haka karamar hukumar ta shirya gudummowar da za ta bayar ga al’ummar da wannan abu ya shafa, sannan kuma ya roki hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa da ta jiha da kuma sauran al’umma da su taimaka wa al’ummar da wannan abu ya shafa.

Mai magana da yawun jami’an tsaro na NSCDC na jihar Jigawa CSC Adamu Shehu, ya tabbatar da faruwar wannan lamari.

Shehu ya ce, gobarar ta kone gidaje hudu kuemus da dabbobi masu yawa da kuma wasu muhimman kayayyaki.

Ya ce, gobarar ba ta kone kowa ba, kuma an samu nasarar kashe ta tun kafin ta yi mummunar barna.

Wannan gobarar ta faru ne, bayan wata da aka yi a wannan yankin wadda ta yi sanadiyyar konewar wasu kauyuka guda uku a  karamar hukumar Kiyawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GobaraJigawaKasuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin Ya Yi Kira Ga Kasashen Da Suka Taba Fama Da Yake-yake Da Su Daidaita Batutuwan Tsaro Da Neman Ci Gaba

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Da Takwaransa Na Ukraine Sun Yi Hira Ta Wayar Tarho

Related

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

2 minutes ago
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet
Labarai

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

45 minutes ago
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

4 hours ago
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

6 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

8 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

9 hours ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Da Takwaransa Na Ukraine Sun Yi Hira Ta Wayar Tarho

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Da Takwaransa Na Ukraine Sun Yi Hira Ta Wayar Tarho

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

August 22, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 22, 2025
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

August 22, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.