• English
  • Business News
Monday, July 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

by Idris Aliyu Daudawa and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu gwamnatin tarayya na fuskantar karin matsin lamba daga bangarori da dama a kan bukatar ta fito da matakai masu muhimmanci na yaki da yunwa a fadin kasar nan. Matsin lamba na baya-bayan nan ya fito ne daga gamayyar kungiyar kwadago na kasa (NLC).

Idan dai ba a manta ba tun 16 ga watan Fabrairu ne kungiyar kwadago ta kasa ta ba da sanarwar zanga- zanga ta kasa baki daya, aka kuma tsaida ranar Talata da Laraba ne saboda nuna gazawar gwamnatin tarayya saboda rashin aiwatar da alkawarin da aka yi da ira ranar 2 ga Oktoba 2023 sanadiyar cire tallafin man fetur.

  • Tinubu Ya Tafi Kasar Qatar Don Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci
  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan

An dauki matakin ne bayan da aka kawo karshen wa’adin mako biyu da aka ba gwamnatin tarayya,ta aiwatar da matakan da za su kawo wa talakawa sauki domin wahalar da suke sha da ta ki ci ta ki cinyewa.

Kungiyar kwadago ta kasa ta fara yajin aikin kwana biyu 27 da 28 ga watan Fabrairu 2024 wanda zai shafin dukkan Jihohi 36 na Nijeriya, tun farko kungiyoyi biyu ne na kwadago suka shirya shiga zanga-zanga ta kwana biyu wato Nigerian Labour Congress da Trade Union Congress,amma daga baya sai kungiyar Trade Union Congress ta fasa shiga cikin Zanga- zangar.

Bugu da kari kungiyoyi masu zaman kansu sun yanke shawarar ba za su cikin zanga-zangar ba, Saboda abinda suka ce wasu bata gari na iya amfani da hakan domin su samu kawo tashin hankali.

Labarai Masu Nasaba

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Kafin fara yin zanga-zangar ta ranar Litinin Jihohin Edo, Osun, da Legas sun fara ne tun ranar Lahadi.

Rahotanni sun nuna yajin aikin ya samu karbuwa sosai a Jihohin Legas ‘yansanda ne suka rika ba masu yin zanga-zangar ruwan sha da biskita, Jihar Borno kuwa ‘yansanda sun hana ‘yan kungiyar kwadago yin zanga-zangar ranar Lahadii ce fadar Shugaban kasa ta ja kunnen kungiyar kwadago ta kasa kada ta yi zanga-zangar kwana biyu wadda za ta karade duk fadin tarayyar Nijeriya, saboda kuncin rayuwa da hauhawar farashin kayan abinci da ke karuwa kowace rana, al’amarin da ya sa ‘yan Nijeriya shiga wani halin ni‘yasu.

Rundunar ‘yansanda ta ja kunne ita ma a kan kada a kawo wata matsalar da za ta shafi yadda ake tafiyar da harkoki lokacin zanga-zangar.

Shugaban kungiyar kwadago na kasa Joe Ajaero shi ya jagoranci dubban ma’aikata da suka shiga Zanga- zangar a Abuja ya ce rayuwar ma’aikata ta sukurkuce domin yanzu ba su iya cin nau’oin abinci da suka saba da su ba don komai ba sai saboda da farashin ya yi tashin gwuron Zabo. Jiya ne dai kungiyar ta janye ci gaba da Zangar-zangar adawa da yadda ‘yan Nijeriya ke fuskantar kuncin rayuwa wanda aka sa ran ci gaba da shi Laraba,an dai sake ba Gwamnatin Tarayya wa’adin mako biyu kwana 14 wanda zai kare ranar 3 ga Maris 2024.

Masu lura da al’amurran yau da kullum sun nuna cewa, har zuwa yanzu matakin da gwamnatin Bola Tinubu take dauka don maganin halin da ake ciki na tsadar rayuwa sun kasa bayyana tasirinsu, domin har yanzu ‘yan Nijeriya ba su ga hatsin da aka yi musu alkawari ba duk da umarnin da shugaban kasa ya bayar ba fito da tan-tan na hatsi don rabawa ga al’umma.

Haka kuma hukumar bayar da agajin gagawa NEMA ta ce ita ma ba ta ga kayan abincin da aka ce za a raba wa mutane ba. Ta yi wannan bayanin ne saboda yadda al’umma ke tururuwa zuwa ofishoshinta neman abin da za su sa a bakin salati.

Duk Da Naira Tiriliyan 5 Da Gwamnoni Suka Karba Har Yanzu Talakawa Na Cikin Wahala
Cire tallafin man fetur da ake sa ran zai fitar da ‘yan Nijeriya da dama daga kangin talauci ta hanyar samun karin kudaden shiga na gwamnatin tarayya da na kananan hukumomi da alama bai yi tasiri ba inda kusan dukkanin jihohin tarayyar kasar nan ba su tabuka komai ba ko kadan, tare da makudan kudaden shigar da suka samu tun daga ranar 29 ga watan Mayu lokacin da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya ayyana cire tallafin.

Sakamakon binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, baya ga kudaden shiga da suke samu a cikin gida da ya kai biliyoyin Naira, jihohin sun samu sama da Naira Tiriliyan 5.108 na kudaden shiga daga Asusun Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa na Tarayya (FAAC) a cikin watanni takwas, daga watan Yulin 2023 (lokacin da aka samu kudaden shiga, domin cire tallafin ya fara ne shiga ne) daga Fabrairun 2024.

Jihohin kasar nan gaba daya kudaden shigar da suka samu sun kai Naira tiriliyan 5,108,219,000,000 (N5.1). da ya hada da Naira tiriliyan 2,690,391,000,000 (Naira 2.69) da suka shigo kai tsaye daga asusun tarayya, da kuma Naira tiriliyan 1,975,899,000,000 da aka raba wa asusun kananan hukumomin da gwamnonin jihohi ke kula da su, da kuma wasu Naira biliyan 441.929 a matsayin kaso 13 cikin 100 na kudaden shiga na ma’adanai da aka raba wa wasu jihohi.

A yayin da cire tallafin ya kara yawan kudin da Asusun Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa na Tarayya (FAAC) ke raba wa a kowane wata zuwa kusan Naira Tiriliyan 1.09 idan aka kwatanta da Naira biliyan 620 da aka yi a baya, gwamnonin jihohin sun gaza wajen inganta rayuwar al’umma da kudin shiga na kowa da kowa na mazauna jihohinsu.

A kidaya ta karshe, kusan jihohi 10 ne suka fara aiwatar da dokar Naira 30,000 da gwamnati ta amince da su a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan gwamnati. Duk da karuwar kudaden shiga, yawancin jihohin har yanzu ba su iya aiwatar da biyan tsohon albashin ba wanda kuma tuni ma’aikata ke neman karin sama da kashi 200 cikin dari.

Lissafin kudaden da Asusun Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa na Tarayya ta ware wa jihohin a tsawon lokacin da ake bitar ta nuna cewa a watan Yuli da aka fara samun kudin shiga na farko bayan tallafin, an raba jimillar kudaden da za a raba kimanin Naira biliyan 907.054 a tsakanin matakai uku na gwamnati, inda jihohin suka dauki kimanin jimillar Naira biliyan 561.49 daga asusun tarayya.

A watan Agusta lokacin da jimillar kudaden shigar da suka hada da Harajin Harajin Daraja, samun kudin canji da kuma kudin musayar kudin lantarki da aka amince a raba su ya kai Naira biliyan 966.110, jihohin sun samu Naira biliyan 591.624.

An samu karuwa a cikin watan Satumba a lokacin da sanarwar Asusun Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Tarayya (FAAC) ya bayyana cewa daga jimillar kudaden shigar da ake rabawa na Naira tiriliyan 1.1 inda gwamnatin tarayya ta samu jimillar Naira biliyan 431.245, jihohin 36 sun samu Naira biliyan 361.188, yayin da kananan hukumomin suka samu Naira biliyan 266.538.

An raba jimillar Naira biliyan 26.473 (kashi 13 na kudaden shiga na ma’adanai) da kuma Naira biliyan 14.657 (kashi 13 na ajiyar da aka samu daga NNPCL) ga jihohin da abin ya shafa a matsayin kudaden shiga.

Haka kuma, daga jimillar kudaden shiga da aka rabawa Naira biliyan 903.480 a watan Oktoban 2023, gwamnatocin jihohi sun samu Naira biliyan 287.071 sannan kuma kananan hukumomi sun samu Naira biliyan 210.900.
An raba jimillar Naira biliyan 84.966 (kashi 13 na kudaden shiga na ma’adanai) ga jihohin da abin ya shafa a matsayin kudaden shiga, wanda ya kawo jimlar kudaden shiga daga asusun tarayya zuwa jihohin zuwa Naira biliyan 582.937.

A ranar 22 ga Nuwamba Asusun Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa na Tarayya (FAAC) ya amince da bayar da Naira biliyan 307.717 ga jihohi, yayin da kananan hukumomin suka samu Naira biliyan 225.209. Naira biliyan 50.674 kuwa (kashi 13 ne na kudaden shiga na ma’adanai) an raba su tsakanin jihohin da abin ya shafa a matsayin kudaden shiga na ion.

FAAC ya kuma raba Naira tiriliyan 1.1 ga dukkan matakan gwamnati a matsayin kudaden shiga daga watan da ya gabata. Sanarwar da aka fitar a karshen taron na wata-wata ta bayyana cewa, yayin da gwamnatin tarayya ta samu jimillar Naira biliyan 402.867, gwamnatocin jihohi kuma sun karbi Naira biliyan 351.697, sannan kananan hukumomi sun samu Naira biliyan 258.810. Jimillar Naira biliyan 75.410 (kashi 13 na kudaden shiga na ma’adanai) an raba wa jihohin da suka amfana a matsayin kudaden shiga na rarar kudaden shiga, kuma hakan ya kara kaso daga kudaden shiga na tarayya.

A watan Janairun 2024 da aka gudanar da taron FAAC na farko na wannan shekarar, an raba Naira tiriliyan 1.127 da aka samu daga kudaden shiga na Disamba. A cikin lissafin da gwamnatin tarayya, ta samu Naira biliyan 383.872, jihohi sun samu Naira biliyan 396.693, kananan hukumomi sun samu Naira biliyan 288.928, sannan jihohin da ake hako mai sun samu Naira biliyan 57.915 a matsayin wani mataki, (kashi 13 na kudaden shiga na ma’adanai).

A karshen kididdigar dai, gwamnatocin jihohin sun karbi Naira biliyan 379.407, da kuma Naira biliyan 278.041 a madadin kananan hukumomi, inda adadin Naira biliyan 85.101 (kashi 13 na kudaden shiga na ma’adinai) su ma suka shigo jihohin da suka amfana a matsayin kudaden shiga na rarar kudaden shiga.

Duk wannan ya biyo bayan biliyoyin da kowace jiha ta samu daga gwamnatin tarayya domin raba wa marasa galihu a cikin al’umma sakamakon tallafin man fetur da kuma tsadar rayuwa da suka biyo baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tsaro Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

Next Post

Sharudda 17 Da Kungiyar Kwadago Ta Gindaya Wa Gwamnati Kafin Janye Zanga-zanga

Related

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
Manyan Labarai

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

1 hour ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

2 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

4 hours ago
Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

5 hours ago
Saurayi Ya Kashe Budurwarsa, Yace Sharrin Ƙwaya Ne
Manyan Labarai

Saurayi Ya Kashe Budurwarsa, Yace Sharrin Ƙwaya Ne

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

18 hours ago
Next Post
NLC

Sharudda 17 Da Kungiyar Kwadago Ta Gindaya Wa Gwamnati Kafin Janye Zanga-zanga

LABARAI MASU NASABA

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

July 21, 2025
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

July 21, 2025
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

July 21, 2025
Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

July 21, 2025
Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

Yadda Gwamnan Katsina Ya Tsira Daga Hatsarin Mota

July 21, 2025
Saurayi Ya Kashe Budurwarsa, Yace Sharrin Ƙwaya Ne

Saurayi Ya Kashe Budurwarsa, Yace Sharrin Ƙwaya Ne

July 21, 2025
Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

July 20, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

July 20, 2025
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

July 20, 2025
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

July 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.