• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ke Kara Ci Gaban Kasashen Afirka

by CMG Hausa
3 years ago

Layin dogo yana daya daga cikin muhimman ababen more rayuwa da kasashen nahiyar Afirka suka amfana da shi, karkashin hadin gwiwar Sin da kasashen na Afirka, baya ga hanyoyin mota, da gadoji na zamani, da makarantu da cibiyoyin lafiya da makamantansu.

Tun bayan kaddamar da layin dogo na zamani na SDR a ranar 31 ga watan Mayun shekarar 2017 tsakanin Mombasa zuwa Nairobo, da kasar Sin ta gina, shekaru biyar da suka gabata, yanzu haka kasar Kenya ta shiga wani sabon tsari na rayuwa, inda ya sauya harkokin sufuri, da kasuwanci da nishadi a kasar Kenya.

Bayanai na nuna cewa, layin dake tafiyar da jiragen kasa na fasinja guda shida a kullum, ya yi nasarar jigilar fasinjoji sama da miliyan 7.7 a cikin shekaru biyar din da suka gabata. Kana a cikin watanni biyar na farkon shekarar 2022, adadin fasinjojin da aka yi jigilar su ta hanyar layin dogon na zamani, ya kai 962,000, wanda ya kai kashi 63 cikin dari a duk shekara.

Haka kuma, a cikin shekaru biyar da suka gabata, layin dogon ya yi jigilar sama da Tan miliyan 1.7 na kwantenoni. Kana yawan kayayyakin da jirgin kasan dakon kaya ya yi jigilarsu a cikin watanni biyar da suka wuce, ya kai tan miliyan 2.54, karuwar kashi 8.3 bisa dari a shekara.

Layin dogon ya kuma samar da wata kafa ga matasan Kenya, wajen bunkasa fasaha da sana’o’insu da samun kudin shiga, da inganta fasaha da samar da aikin yi da raya manyan sassan tattalin arzikin kasar kamar aikin gona, da masana’antu da yawon shakatawa.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Baya ga layin dogo tsakanin Mombasa da Nairobi, akwai na Tanzaniya zuwa Zambia (Tazara) da wadanda Sin ta gina a sassan daban-daban na Najeriya da sauran kasashen Afirka, kuma duk sun taimaka wajen saukaka jigilar jama’a da hajoji tsakanin kasashen nahiyar, baya da samar da guraben ayyukan yi da karin kudaden shiga ga mazauna wadannan yankuna, galibi matasa.

Sabon dakin taro na zamani da kasar Sin ta samar da kudin ginawa da aka kaddamar a Zambia a baya-bayan nan, ya kara nuna cewa, alakar Sin da Afirka, alaka ce ta amintakar kut-da kut da mutunta juna da samun nasara tare. Kuma duk kokarin da wasu kasashen yamma ke yi na neman illata wannan dangantaka, ba zai taba yin nasara ba. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika
Daga Birnin Sin

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Kai Samame A Sansanin Bayar Da Horo Na Kungiyar IPOB Sun Kashe 3

Jami'an Tsaro Sun Kai Samame A Sansanin Bayar Da Horo Na Kungiyar IPOB Sun Kashe 3

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.