• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

by Rabi'at Sidi Bala
5 months ago
Kannywood

Tun bayan daura auren mawaki Dauda Adamu Kahutu Rarara da amaryarsa jaruma kuma mawakiya Aisha Humaira ake ci gaba da tattaunawa kan bikin a kafofin sadarwa musamman bayan shagalin cin abincin dare na bikin da aka yi a Jihar Kano.

Daga cikin abubuwan da suka dauki hankali sun hada da adon da amarya da ango suka sha, kwalliyar da aka yi a zauren walima da kuma manyan bakin da suka halarci shagulgulan bikin a mabanbantan lokuta, biki ne da aka yi na kasaita musamman ganin yadda Rarara ke jan zarensa a wannan lokaci har ma wasu ke kwatanta shi da shahararrun mawakan kasar Hausa da suka shude, sanadiyyar baje-kolin basirar da yake yi a cikin wakokinsa.

  • Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
  • Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

A wani rahoto da BBC Hausa ta fitar mun tsakuro maku yadda jarumai da mawaka a masana’antar Kannywood suka auri junansu, dukkan wadannan aurarrakin anyisu cikin annashuwa da kaunar juna, akwai wadanda suke har yanzu a matsayin ma’aurata yayinda wasu kuma mai rabawa ta raba.

 

Dauda Adamu Rarara da Aisha Humaira

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

A ranar Juma’a, 25 ga watan Afrilun shekarar 2025 ce aka daura auren Dauda Kahutu Rarara da amaryarsa Aisha Ahmad wadda aka fi sani da Aisha Humaira a birnin Maiduguri da ke Jihar Borno, an dade ana rade-radin akwai soyayya tsakanin ma’auratan biyu, amma a duk lokacin da aka tambaye su, sai su ce aiki da ne ya hadasu ba wani abu ba.

A shekarar da ta gabata Rarara ya rera wata waka mai taken ‘Aisha’, wadda a ciki ya baza kalaman soyayya har aka yi ta cewa da ita yake yi, amma sai aka yi amfani da wakar a fim din da ita jarumar ta shirya mai suna ‘A cikin biyu’ wanda Ali Nuhu ya hau a matsayin mijinta a wannan shirin.

Daga cikin wadanda suka halarci daurin auren akwai jiga-jigan yan siyasa irin su tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari da mataimakin shugaban majalisar Dattawan Nijeriya Sanata Barau Jibrin da sauransu.

 

Abubakar Bashir Maishadda da Hassana Muhammad

Daya daga cikin masu shirya fina-finai a masana’antar Kannywood Abubakar Bashir Maishadda wanda ake wa lakabi da ‘king of bod office’ saboda yadda yafi mayar da hankali wajen haska fina finansa a gidajen sinima.

Furodusan ya auri jaruma Hassana Muhammad, wadda ta fito a matsayin babbar jaruma a wasu fina-finan kamfaninsa, ciki har da shirin Hauwa Kulu da sauransu, an daura aurensu ne a ranar Lahadi, 13 ga watan Maris na shekarar 2022 a Masallacin Murtala da ke Kano.

Maishadda ya yi aure ne a lokacin da finafinansa suke tashe a masana’antar, inda yake fitar da fina-finai manya tare da jarumai mata da suke tashe a wannan lokacin, hakan ya sa aka rika alakanta shi da jarumai mata da yawa da suke fitowa a finafinansa.

 

Sani Danja da Mansurah Isah

Daya daga cikin auren yan Kannywood da ya kasance daya tamkar da goma kuma akayi bikin da za a dade ba a manta da shi ba shi ne na taurari biyu da suke tashe a lokacin da suka yi aure, wato Sani Musa Danja da Mansurah Isah, a ranar 14 ga watan Yuli na shekarar 2007 ne aka yi bikin auren jaruman, inda aka gudanar da biki na kece raini da kasaita.

Sani Danja ya yi tashe a shekarun baya hakazalika ya samu farin jini wurin ‘yanmata inda aka rika alakanta shi da taurari mata daban daban, daya daga ciki da ta yi fice ita ce Maryam Jan kunne, amma daga bisani ya rufe kunnensa ya zabi Mansurah Isah domin ta zama uwar ‘ya’yansa.

Sani Danja da Mansurah suna cikin yan fim na farko-farko da suka auri juna, kuma suka dade suna tare kafin auren ya mutu a shekarun baya, Allah ya albarkaci auren da yaya hudu mace daya Iman sai kuma maza uku da suka hada da Khalifa, Sultan sai kuma dan autansu Sudais.

 

Ummi Rahab da Lilin Baba

Wani auren da ya janyo muhawara a shafukan sada zumunta shi ne na Ummi Rahab da angonta Lilin Baba, Ummi ta taso cikin masana’antar Kannywood a matsayin ta hannun damar babban tauraro Adam A. Zango, tun daga fim din da ta fara fitowa wato ‘Ummi’, a lokacin da Ummi ta nuna zata auri Lilin Baba an yi ta rade-radin cewa Adam Zango bai so hakan ba, sai dai duk da haka an daura auren kuma Ummi da Lilin Baba na ci gaba da zamansu a matsayin mata da miji.

Yayin da wasu ke zargin Ummi Rahab da juya wa wanda ya raine ta a masana’antar baya, wasu kuma sun zargi Zango da kokarin hana matashiyar rawar gaban hantsi, an daura auren Ummi Rahab da Lilin Baba a ranar Asabar 18 ga watan Yulin shekarar 2022 a Tudun Murtala da ke Kano.

 

Fati Muhammad da Sani Mai Iska

Wadanda suka dade su na bibiyar harkokin fim din Hausa sun san irin tashen da Fati Muhammad ta yi, a matsayin daya daga cikin taurari mata na farko-farko da tauraruwarsu ta haska a shekarun baya a masana’antar Kannywood, wasu ma na ganin cewa ya zuwa wannan lokaci babu tauraruwar da ta shiga zukatan masu kallo kamar yadda Fati Muhammad ta yi a lokacin da take zamaninta.

Auren jarumar da Sani Mai Iska ya bai wa mutane da dama mamaki kasancewar an fi alakanta ta da wasu daban kamar Ali Nuhu duba da cewar sun yi zamani a tare inda suka fito a manyan fina finai da dama kamar Sangaya da Mujadala, aurenta da Sani Mai Iska ya ci gaba da jan hankali musamman ganin yadda suka bar kasar zuwa Birtaniya bayan auren domin cin amarci a can.

 

Ahmed S. Nuhu da Hafsat Shehu

Wani aure da ya dade a zukatan masoyan fina-finan Huasa shi ne wanda aka yi tsakanin jarumi Ahmed S Nuhu da abokiyar aikinsa Hafsat Shehu, masoyan biyu sun kasance abin so ga mutane da dama da ke kallon fina-finan Hausa na wancan lokacin, hakan bai rasa nasaba da shaidar da aka yi wa Ahmed na kasancewa mai son zaman lafiya da iya zama da mutane a ciki da wajen masana’antar.

A bangare daya Hafsat kan fito a yawancin fina-finai a matsayin mai sanyin zuciya da fara’a, lamarin da ya sa take burge masu kallo, tauraruwar ta fara tashe ne bayan fim dinta na Zabari ta kamfanin FKD ya shirya, sai dai auren bai dade ba, kasancewar Ahmed ya rasu a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2007 sakamakon hatsarin mota da ya rutsa dashi a garin Azare na Jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriya.

 

Shu’aibu Lawan Kumurci Da Balaraba Muhammad

Wani babban al’amari da ya faru a shekarun baya a masana’antar Kannywood shi ne aure tsakanin jarumi Shuaibu Lawan Kumurci da Balaraba Muhammad wanda a wancan lokacin ya zama daya daga cikin auratayya ta farko-farko da aka kulla a tsakanin jaruman masana’antar.

Duk cewa auren bai dade ba Allah ya dauki rayuwar Balaraba, amma dai auren ya kasance wanda aka dade ana mamakinsa a Kannywood duba da cewar ana yi wa Kumurci kallon irin mutanen nan masu zafi yayin fitowa a cikin fina-finai, ba kamar Balaraba wadda da dama ke gani a matsayin mace mai sanyin hali ba.

 

Wasila Isma’il da Al’amin Ciroma

Fim din Lerawa Production da ake kira Wasila, shi ne ya fito da Wasila Isma’il a duniyar fim din Hausa, aurenta da Al’amin Ciroma ya ja hankali sosai, duk da cewa a lokacin ba a samu yawaitar kafofin sada zumunta irin yanzu ba, auren ya dauki hankali ne saboda ya zo a daidai lokacin da masu kallon fina-finan Hausa suke ci gaba da tattaunawa game da fim din ‘Wasila’

Wasila Isma’il wadda ta fito a matsayin matar Ali Nuhu cikin fim ɗin ‘Wasila’ bayan tafka soyayya mai ratsa zukata, ta jefa masu kallo cikin jimami bayan cin amanar Jamilu da wani tsohon abokinta mai suna Moda, soyayyar Wasila da Jamilu na daga cikin soyayya mafi zafi da aka taba gani a duniyar fina-finan Hausa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Next Post
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.