• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Tinkarar Sauyin Yanayi A Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
Sauyin yanayi

A yayin da matsalar sauyin yanayin duniya ke kara kamari, ya zama dole kasa da kasa su sa kaimin amfani da makamashi masu tsabta da ake iya sabuntawa, a wani kokari na tinkarar matsalar sauyin yanayi, da ma tabbatar da dauwamammen ci gaba. Don haka, a kwanan baya, a gun taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 28(COP28) da ke gudana a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa, sama da kasashen duniya 100 ne suka amince da manufar ninka adadin wutar lantarki da ake samarwa, da nau’o’in makamashi da ake iya sabuntawa nan zuwa shekarar 2030. 

Wasu daga cikin kafofin watsa labarai da suka yi tsokaci kan hakan, sun ce kasar Sin ce daya tilo, cikin manyan kasashen duniya, da ke da ainihin ikon cimma wannan buri.

  • COP28: Sin Da Afirka Za Su Bunkasa Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kananan Ayyukan Samar Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Hasali ma dai, furucin ba wai an yi shi ne ba tare da tushe ba. Kasancewar kasar Sin ta dade tana dora matukar muhimmanci a kan bunkasa makamashi masu tsabta, wadda a shekaru bakwai a jere ta zo na farko a duniya wajen yawan zuba jari ta bangaren samar da makamashi masu tsabta, sa’an nan, ta kuma zo ta farko a duniya wajen samar da wutar lantarki da makamashi masu tsabta, adadin da ya zarce KW biliyan 1.4. Baya ga haka, sama da rabin motoci masu aiki da sabbin makamashi masu tsabta na duniya a kasar Sin suke. Lallai, ma iya cewa, batun rage fitar da iskar Carbon ya zame wa al’ummar Sinawa jini da tsoka.

A sa’i daya kuma, kasar Sin tana kokarin taimakawa kasa da kasa wajen bunkasa makamashi masu tsabta. A gun hadaddiyar daular Larabawa da ke karbar bakuncin taron COP28, akwai wata tashar samar da wuta da makamashin rana da ta kasance irinta mafi girma a duniya, wadda wani kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin ginawa, tashar da ake kira Al Dhafra. An ce, tashar na iya biyan bukatun magidanta kimanin dubu 200, wadda kuma za ta rage iskar Carbon da ake fitarwa da kimanin ton miliyan 2.4, kwatankwacin yawan iskar Carbon da motoci dubu 500 ke fitarwa.

Sai kuma a Nijeriya, tashar samar da wuta da karfin ruwa ta Zungeru, wadda ba da jimawa ba kamfanin kasar Sin da ya gina ta ya mikawa kasar ta Nijeriya, wadda ta kasance daya daga cikin tashoshin irinta mafiya girma a kasar, wadda wutar lantarki da ta samar har ta ishi birane biyu masu girman Abuja, inda ta taka muhimmmiyar rawa wurin daidaita matsalar karancin wuta da ake fuskanta a kasar.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Da tashar Al Dhafra da ta Zungeru, da ma tashar Karot ta kasar Pakistan, kusan muna iya samun irin aikin samar da makamashin da ake iya sabuntawa da kamfanonin kasar Sin ke aiwatarwa ko ina a duniya. Kawo yanzu, rabin na’urorin samar da wutar lantarki da karfin iska, da ma kaso 80 na na’urorin samar da wuta da makamashin rana a kasar Sin ce ake samar da su.

Daidai kamar yadda Abdulaziz Alobaidli, babban jami’in kamfanin Masdar na samar da makamashi masu tsabta na hadaddiyar daular Larabawa ya fada, Sin babbar kasa ce da ke sauke nauyin da ke bisa wuyanta, wadda ta yi namijin kokarin bunkasa aikin samar da makamashi masu tsabta, wadda kuma ta ba da gudummawarta wajen tinkarar matsalar sauyin yanayi a duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.