• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Tinkarar Sauyin Yanayi A Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Tinkarar Sauyin Yanayi A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da matsalar sauyin yanayin duniya ke kara kamari, ya zama dole kasa da kasa su sa kaimin amfani da makamashi masu tsabta da ake iya sabuntawa, a wani kokari na tinkarar matsalar sauyin yanayi, da ma tabbatar da dauwamammen ci gaba. Don haka, a kwanan baya, a gun taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 28(COP28) da ke gudana a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa, sama da kasashen duniya 100 ne suka amince da manufar ninka adadin wutar lantarki da ake samarwa, da nau’o’in makamashi da ake iya sabuntawa nan zuwa shekarar 2030. 

Wasu daga cikin kafofin watsa labarai da suka yi tsokaci kan hakan, sun ce kasar Sin ce daya tilo, cikin manyan kasashen duniya, da ke da ainihin ikon cimma wannan buri.

  • COP28: Sin Da Afirka Za Su Bunkasa Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kananan Ayyukan Samar Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Hasali ma dai, furucin ba wai an yi shi ne ba tare da tushe ba. Kasancewar kasar Sin ta dade tana dora matukar muhimmanci a kan bunkasa makamashi masu tsabta, wadda a shekaru bakwai a jere ta zo na farko a duniya wajen yawan zuba jari ta bangaren samar da makamashi masu tsabta, sa’an nan, ta kuma zo ta farko a duniya wajen samar da wutar lantarki da makamashi masu tsabta, adadin da ya zarce KW biliyan 1.4. Baya ga haka, sama da rabin motoci masu aiki da sabbin makamashi masu tsabta na duniya a kasar Sin suke. Lallai, ma iya cewa, batun rage fitar da iskar Carbon ya zame wa al’ummar Sinawa jini da tsoka.

A sa’i daya kuma, kasar Sin tana kokarin taimakawa kasa da kasa wajen bunkasa makamashi masu tsabta. A gun hadaddiyar daular Larabawa da ke karbar bakuncin taron COP28, akwai wata tashar samar da wuta da makamashin rana da ta kasance irinta mafi girma a duniya, wadda wani kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin ginawa, tashar da ake kira Al Dhafra. An ce, tashar na iya biyan bukatun magidanta kimanin dubu 200, wadda kuma za ta rage iskar Carbon da ake fitarwa da kimanin ton miliyan 2.4, kwatankwacin yawan iskar Carbon da motoci dubu 500 ke fitarwa.

Sai kuma a Nijeriya, tashar samar da wuta da karfin ruwa ta Zungeru, wadda ba da jimawa ba kamfanin kasar Sin da ya gina ta ya mikawa kasar ta Nijeriya, wadda ta kasance daya daga cikin tashoshin irinta mafiya girma a kasar, wadda wutar lantarki da ta samar har ta ishi birane biyu masu girman Abuja, inda ta taka muhimmmiyar rawa wurin daidaita matsalar karancin wuta da ake fuskanta a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa

Da tashar Al Dhafra da ta Zungeru, da ma tashar Karot ta kasar Pakistan, kusan muna iya samun irin aikin samar da makamashin da ake iya sabuntawa da kamfanonin kasar Sin ke aiwatarwa ko ina a duniya. Kawo yanzu, rabin na’urorin samar da wutar lantarki da karfin iska, da ma kaso 80 na na’urorin samar da wuta da makamashin rana a kasar Sin ce ake samar da su.

Daidai kamar yadda Abdulaziz Alobaidli, babban jami’in kamfanin Masdar na samar da makamashi masu tsabta na hadaddiyar daular Larabawa ya fada, Sin babbar kasa ce da ke sauke nauyin da ke bisa wuyanta, wadda ta yi namijin kokarin bunkasa aikin samar da makamashi masu tsabta, wadda kuma ta ba da gudummawarta wajen tinkarar matsalar sauyin yanayi a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yobe: Za A Rataye Sojan Da Ya Harbe Malamin Addini

Next Post

Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

Related

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

27 minutes ago
Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa
Daga Birnin Sin

Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa

11 hours ago
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
Daga Birnin Sin

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

18 hours ago
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
Daga Birnin Sin

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

19 hours ago
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
Daga Birnin Sin

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

20 hours ago
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

22 hours ago
Next Post
Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Da Kin Amincewar Amurka Da Kudurin Tsagaita Wuta Domin Jin Kai

LABARAI MASU NASABA

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

May 31, 2025
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

May 31, 2025
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.