• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 hours ago
Sin

Kasar Sin da gaske take yi game da kudurinta na fifita rayuwar jama’arta a gaba da komai, kamar yadda take ci gaba da auna ci gabanta ta fuskoki da dama a kan mizanin kare hakki da mutuncin kowane dan kasa.

 

Yanzu haka, kasar ta dauki wani kwakkwaran mataki na sake fasali tare da shigar da tsarin kare muradun jama’a a cikin dokokin shari’ar kasar a hukumance, da nufin karfafa kare muradun kasa da na zamantakewa. A karkashin haka, an gabatar da wani daftarin doka a ranar Jumma’ar da ta gabata ga babban kwamitin Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Sin (NPC) domin amincewa da shi.

  • DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta
  • Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

Dokar da ake son kafawa ta kunshi karfafa sa ido kan shari’a da kuma zamanintar da yadda ake gudanar da shugabancin al’amuran jama’a. Shugaban kwamitin kula da harkokin shari’a na NPC Yang Xiaochao ya ce, dokar tana da muhimmanci wajen kare muradun jama’a da kuma karfafa ci gaban da aka samu tun bayan kaddamar da amfani da wani tsarin kare muradun jama’a a shekarar 2015.

 

LABARAI MASU NASABA

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

Asalin tsarin shari’ar da ake amfani da shi game da kare muradun al’umma ya bai wa masu gabatar da kara damar yin aiki na neman hukunta masu laifi a madadin sauran al’umma a shari’o’in da suka shafi laifukan gurbata muhalli, da rashin kiyaye tsaftar abinci, da kuma rashin da’a ga gwamnati wadanda dukkansu idan aka bar su kara-zube, za su tauye hakkokin galibin jama’a. Amma a halin yanzu, sabon daftarin dokar da ake son kafawa ya fayyace nau’ikan dokoki 16, ciki har da karin wasu muhimman abubuwa guda biyu da suka shafi al’adun gargajiya da kuma tsaron kasa, wanda ke nuna kara fadada tsarin dokar.

 

Domin ganin ba a tauye hakkin kowane bangare tsakanin mahukunta da mabiya ba, a karkashin daftarin dokar, dole ne masu gabatar da kara su fara gabatar da bukatar hukumomin gwamnati da su sauke nauyin da ke wuyansu kafin shigar da kara a kansu. A bangaren kare hakkin jama’a kuma, an haramta daukar matakan tilastawa kamar hana mutum amfani da asusunsa na banki da kadarori ko takaita ‘yancin walwala a yayin gudanar da bincike. Kazalika, an karfafa gwiwar ‘yan kasa da kungiyoyin kyautata zamantakewa su bayar da rahoton keta hakkokin jama’a da kuma sa ido kan shari’o’in da ake gudanarwa kan hakan.

 

Daga shekarar 2015 zuwa 2025, hukumomin da ke kula da share hawayen jama’a a bangaren shari’a sun yi aiki a kan korafe-korafe fiye da miliyan 1.22 wadanda galibi aka gabatar a kan ma’aikatun gwamnati.

 

Su dai tsare-tsaren da ake amfani da su na kare muradun jama’a a kasar Sin ba a tattare suke a wuri guda ba, suna warwartse ne a karkashin dokokin gudanarwa na fararen hula daban-daban, amma wannan daftari ya hade su wuri guda.

 

Kokarin tabbatar da wannan daftarin doka na kare muradun al’umma a kasar Sin, babu shakka ya kara fito da burin kasar na gyare-gyare a dukkan fannoni tare da cike gibin da ake ganowa, yayin da kasar ta hau turbar cimma burin zamanintarwa a karkashin tsarin gurguzu nan da shekarar 2035. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki
Daga Birnin Sin

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Next Post
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami'in INEC

LABARAI MASU NASABA

Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.