ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda kasar Sin Ta Cika Alkawuranta A Harkokin Diplomasiyya

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sin

Ziyarar shugaban kasar Sin Xi Jinping a yankin Latin Amurka, tare da halartar taron shugabannin tattalin arzikin kungiyar APEC da taron kolin G20 da aka gudanar, ya da jawo hankalin kasa da kasa. Yayin ziyararsa, Xi Jinping tare da takwararsa ta kasar Peru Dina Boluarte sun halarci bikin kaddamar da tashar ruwa ta Chancay ta Peru ta kafar dibiyo, inda aka shaida yadda aka tabbatar da shawarar “ziri daya da hanya daya” a kasar Peru, da ma yadda kasar Sin ta cika alkawarin da ta dauka da sauran kasashe.

 

Ba wannan ziyara kadai ke iya bayyana sahihancin kasar Sin a wajen aiwatar da harkokin diplomasiyya ba. Tabbatar da ayyuka 8 na inganta raya shawarar “ziri daya da hanya daya” da tabbatar da manyan ayyuka 10 na hadin gwiwar Sin da Afirka wajen zamanintar da kansu, da kuma tabbatar da ayyuka 8 na karfafa raya duniya baki daya da sauransu, mun iya gano cewa, shugaba Xi Jinping ya sha ambata “tabbatar da ayyuka” a cikin jawaban da ya gabatar a tarukan duniya. Sin tana nacewa ga daukar ainihin matakai don tabbatar da hadin gwiwar cin moriyar juna. Alal misali, a karkashin shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, kamfanoni Sin sun taimakawa kasashen Afirka wajen gina layin dogo da tsawonsa ya kai kilomita dubu 10 da hanyoyin mota masu nisan kilomita dubu 100. Layin dogo da ke tsakanin Mombassa da Nairobi na Kenya, da kuma layin dogo dake tsakanin Habasha da Djibouti, kana da layin dogo dake tsakanin Abuja da Kaduna na Najeriya da dai sauran ayyukan da kamfanonin Sin suka ba da taimakon gina su, na taimaka wa kasashen Afirka wajen kafa tsarin layukan dogo. Bayan wannan, bikin baje kolin kayayyakin da Sin ke shigowa da su daga ketare wato CIIE ya samar wa kamfanonin kasa da kasa damar shiga kasuwannin kasar Sin, don more damammaki da moriyar tsarin dunkulewar duniya baki daya. Kazalika, asusun raya duniya da hadin gwiwar kasashe masu tasowa ya samar wa ayyuka fiye da 150 tallafi.

ADVERTISEMENT

 

Kyan alkawari cikawa, yadda kasar Sin ke yi ke nan a wajen aiwatar da harkokin diplomasiyya da kasa da kasa, wanda hakan ya zama alamar da ta yi shuhura da ita a wannan bangare. Hakan ya sa Sin ta samu karin amincewa daga kasashen duniya, har ta karfafa kwarin gwiwa da hadin kai a tsakanin kasa da kasa wajen gina kyakkyawar makomar duniya. (Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Matan Annabi Muhammadu (SAW)

Matan Annabi Muhammadu (SAW)

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.