• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ta Yi Nasarar Saukaka Fatara Da Raya Karkara A Gomman Shekaru

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ta Yi Nasarar Saukaka Fatara Da Raya Karkara A Gomman Shekaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa Sin kasa ce wacce ta dauki yaki da fatara da muhimmanci, musanmman ma a yankunan karkara inda masu fama da kangin talauci suka fi yawa. Sin dai kasa ce mai tasowa da ta fi kowace girma a duniya kuma tana gaba-gaba a kan yaki da fatara ko kuma talauci a yayin da ta dauki matakai wadanda suka sa ta kawar da kangin talauci daga dukkan fannoni zuwa shekarar 2020.

Wannan cimma nasara dai yana da inganci mai yawa a rayuwar jama’a, da tattalin arziki, da yanayin tsarin gudanar da mulki.

Matakan dai da aka fi ba da muhimmanci a yaki da fatara da raya karkara su ne kamar: fifita harkar noma a kasafin kudi na kasa, da tallafi ga manoma da masu fama da fatara, da bayar da bashi maras yawan riba, da cire haraji a kan manoma da kayan amfanin gona, da bada tallafi a kan kayan aikin gona da kuma saukaka biyan kudi daga ’yan makaranta na karkara. Ana kuma shawartar manoma da su rika shiga kungiyoyin hadin gwiwa domin samun ci gaba da kuma bunkasa jarinsu.

A cikin hanyoyin da tsarin ya kunsa dai sun hada da zuba jari da bunkasa ababen more rayuwa da bunkasa fannin noma da bada tallafi, da bada basusssuka marasa kudin ruwa, haka kuma gwamnati na fadakar da manyan kamfanoni da su zuba jari su hada kai da kananan ’yan kasuwa musamman wadanda ke karkara. Lallai abin jinjinawa ne yadda wannan shiri ya yi nasara a kan saukaka fatara da kuma raya karkara a cikin shekaru goman da suka wuce.

A shekarun baya dai lokacin da na samu damar kai ziyara kasar Sin a yayin da na je wasu larduna wadanda suka hada da Beijing, da Shanghai, da Anhui, da Jiangsu, da Fujian, da Shaanxi.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Abubuwan da suka fi burge ni a shirin yaki da fatara na kasar Sin a nan shi ne kokarin da samari da suka kammala karatun jami’o’i suke yi a kan wani shiri wanda aka dauka su domin aiki da taimakawa a kauyuka don ganin iyalai masu fatara su samu kudaden shiga ta hanyoyi da dama musamman noma, da kiwon dabbobi, da sana’o’i domin fitar da su daga kuncin fatara.

Wani abun burgewar kuma da na lura da shi a cikin ziyarce-ziyarce na a cikin kasar shi ne wato, manoma ba su biyan kudi a manyan hanyoyi wato “toll gate” in dai har sun dauko kayan amfanin gona. Suna wucwe ne kyauta, kuma wannan duk yana cikin tsarin tallafi da rage fatara ne.
Bugu da kari, a sakamakon wannan nauyi da jam’iyyar Kwaminis ta kasar ta dauka, an samu cimma nasarar saukaka fatara da kuma bunkasa yankunan karkara a gomman shekarun da suka gabata a karkashin shirin, wanda aka ayyana a taro na kasa na 18 na jam’iyyar Kwaminis ta kasar a shekarar 2012.

A wannan lokaci ne aka kaddamar da shirin kuma aka tashi gaba daya domin cimma nasarar kakkabe fatara wanda a karshe aka yi nasarar fitar da mutanen da talaucin ya yi ma katutu fiye da miliyan 100. A nan dai ina iya cewa samar da abinci ta fannin fadada harkar noma da raya karkara ne babbar nasara domin a yau, kasar Sin tana ci da kanta duk da tana da yawan mutanen da ya kai biliyan 1.4, dan haka kuma ana samun karin ci gaba a kauyuka.

A sakamakon nasarar da kasar Sin ta samu na cimma burinta na kawar da talauci da raya karkara, kasashen Afirka ma za su iya koyi da matakan da kasar Sin ta dauka domin saukaka fatara a kasashensu.

A Najeriya, a misali, gwamnati ta dauki irin wannan darasi a yayin da ta bullo da shirin bunkasa noman shinkafa ta hanyar bayar da basussuka masu karamar riba da tallafi ga manoma ta hanyar samar da kayan aikin gona da takin zamani. Ta wannan darasi, manoma da dama sun samu ci gaba kuma kasar Najeriya ta samu bunkasar tattalin arziki da kuma rage kudin fita da ake amfani da su wajen shigowa da shinkafar a shekarun baya. (Mai sharhi: Lawal Sale)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalaman Xi Jinping Game Da Kishin Kasa

Next Post

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

15 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

16 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

18 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

18 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

20 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

21 hours ago
Next Post
Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

Gwamnonin APC Suna Goyan Bayan Osinbajo A Zaben Fidda Gwani

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.