• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kudin Sin Ke Samun Karin Karbuwa A Kenya

by CMG Hausa
2 years ago
Sin

Yayin da kasashen duniya da dama ke kara bayyana bukatar fadada cudanya, da hada-hadar kasuwanci ta amfani da kudaden cikin gida, maimakon nacewa amfani da dalar Amurka, yanzu haka a kasar Kenya dake gabashin Afirka wannan buri ya fara ciki, inda kudin kasar Sin RMB ke kara samun karbuwa tsakanin al’ummun kasar musamman ’yan kasuwa dake gudanar da cinikayya da takwarorinsu na kasar Sin.

Ko shakka babu, hakan wata manuniya ce dake tabbatar da cewa, sannu a hankali, kudin Sin RMB na maye gurbin dalar Amurka, a hada hadar kasuwanci dake kara bunkasa tsakanin kasashen biyu.

  • Sin Ta Mikawa Gwamnatin Sudan Kashin Farko Na Tallafin Jin Kai 

Wasu alkaluman hukumar kididdiga ta kasar sun nuna cewa, kasar Sin ce babbar abokiyar huldar cinikayyar kasar Kenya, kasancewarta mafi zuba jarin waje, da gudanar da ayyukan raya kasa a Kenya, idan an kwatanta da sauran kasashe dake gudanar da irin wadannan huldodi tare da kasar.

A shekarar 2022 da ta gabata kadai, alkaluman hukuma sun nuna cewa, adadin hajojin da Kenya ta fitar zuwa Sin sun kai darajar kudin kasar Shillings biliyan 27.5, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 193, yayin da adadin hajojin Sin da kasar ta shigar gida suka kai darajar dalar Amurka biliyan 3.17.

Sakamakon irin wannan cudanyar kasuwanci mai armashi dake wanzuwa tsakanin kasashen biyu, a halin da ake ciki, bankunan kasuwanci da dama a Kenya, suna samar da damar hada-hada da kudin Sin RMB, wanda a baya babu irin wannan dama. Hakan ya nuna irin ci gaban da aka samu, karkashin manufar amfani da kudaden gida mafiya sauki domin habaka cinikayya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Masharhanta na cewa, amfani da kudade daban daban na kasashen dake cudanyar kasuwanci da juna, muhimmin mataki ne na bunkasa alakar cinikayya, saboda hakan yana iya rage tsadar hada-hada, ta hanyar kawar da bukatar canjin kudi zuwa dalar Amurka, ko sauran kudaden manyan kasashen yammacin duniya.

Idan har wannan manufa ta dore, ko shakka babu karin kasashe masu tasowa, musamman na nahiyar Afirka, za su ci babbar gajiya daga hada-hada da kudin kasar Sin RMB, yayin da Sin da kasashen na Afirka ke kara fadada hada-hadar kasuwanci da cinikayya a dukkanin fannoni. (Saminu Hassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Katsina Ta Amince Da Raba Hatsi Da Takin Zamani Don Tallafawa 

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Katsina Ta Amince Da Raba Hatsi Da Takin Zamani Don Tallafawa 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.