• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kudin Sin Ke Samun Karin Karbuwa A Kenya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kudin Sin Ke Samun Karin Karbuwa A Kenya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasashen duniya da dama ke kara bayyana bukatar fadada cudanya, da hada-hadar kasuwanci ta amfani da kudaden cikin gida, maimakon nacewa amfani da dalar Amurka, yanzu haka a kasar Kenya dake gabashin Afirka wannan buri ya fara ciki, inda kudin kasar Sin RMB ke kara samun karbuwa tsakanin al’ummun kasar musamman ’yan kasuwa dake gudanar da cinikayya da takwarorinsu na kasar Sin.

Ko shakka babu, hakan wata manuniya ce dake tabbatar da cewa, sannu a hankali, kudin Sin RMB na maye gurbin dalar Amurka, a hada hadar kasuwanci dake kara bunkasa tsakanin kasashen biyu.

  • Sin Ta Mikawa Gwamnatin Sudan Kashin Farko Na Tallafin Jin Kai 

Wasu alkaluman hukumar kididdiga ta kasar sun nuna cewa, kasar Sin ce babbar abokiyar huldar cinikayyar kasar Kenya, kasancewarta mafi zuba jarin waje, da gudanar da ayyukan raya kasa a Kenya, idan an kwatanta da sauran kasashe dake gudanar da irin wadannan huldodi tare da kasar.

A shekarar 2022 da ta gabata kadai, alkaluman hukuma sun nuna cewa, adadin hajojin da Kenya ta fitar zuwa Sin sun kai darajar kudin kasar Shillings biliyan 27.5, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 193, yayin da adadin hajojin Sin da kasar ta shigar gida suka kai darajar dalar Amurka biliyan 3.17.

Sakamakon irin wannan cudanyar kasuwanci mai armashi dake wanzuwa tsakanin kasashen biyu, a halin da ake ciki, bankunan kasuwanci da dama a Kenya, suna samar da damar hada-hada da kudin Sin RMB, wanda a baya babu irin wannan dama. Hakan ya nuna irin ci gaban da aka samu, karkashin manufar amfani da kudaden gida mafiya sauki domin habaka cinikayya.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Masharhanta na cewa, amfani da kudade daban daban na kasashen dake cudanyar kasuwanci da juna, muhimmin mataki ne na bunkasa alakar cinikayya, saboda hakan yana iya rage tsadar hada-hada, ta hanyar kawar da bukatar canjin kudi zuwa dalar Amurka, ko sauran kudaden manyan kasashen yammacin duniya.

Idan har wannan manufa ta dore, ko shakka babu karin kasashe masu tasowa, musamman na nahiyar Afirka, za su ci babbar gajiya daga hada-hada da kudin kasar Sin RMB, yayin da Sin da kasashen na Afirka ke kara fadada hada-hadar kasuwanci da cinikayya a dukkanin fannoni. (Saminu Hassan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dauda Ya Karbi ‘Yan Mata Hudu Da Suka Kwashe Watanin 7 A Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Next Post

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Katsina Ta Amince Da Raba Hatsi Da Takin Zamani Don Tallafawa 

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

32 minutes ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

2 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

3 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

19 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

20 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

22 hours ago
Next Post
Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Katsina Ta Amince Da Raba Hatsi Da Takin Zamani Don Tallafawa 

Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Katsina Ta Amince Da Raba Hatsi Da Takin Zamani Don Tallafawa 

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Sin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.