• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

by Sani Anwar, Abdullahi Muh'd Sheka, Muhammad Awwal Umar, Zubairu M Lawal, Shehu Yahaya, El-Zaharadeen Umar, Munkaila T. Abdullahi and Umar Faruk
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata matsala da ke kunno kai tare da yin barazana ga harkokin noma a halin yanzu ita ce, batun mayar da gonaki zuwa filaye ko gidajen kwana a kafatanin jihohin Arewacin wannan kasa baki-daya.

Har ila yau, wannan dalili ne ya sa wakilanmu daga wasu jihohi na Arewacin kasar, suka tattara mana rahotanni ta hanyar tattaunawa da wadanda abin ya shafa, domin kokarin lalubo bakin zaren; ta hanyar jin alfanu da kuma rashin alfanu na wannan dambarwa, inda wasu suka goyi bayan mayar da filayen gonaki, wasu kuma suka soki yin hakan.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka

Ga dai rahotannin da wakilan namu suka aiko mana da su:

Kano

Batun sayar da gonakin noman abinci, musamman ga masu karamin karfin da suke noma dan wani abu daga cikin abincin da suke amfani da shi a gidajensu, yanzu haka ana iya cewa; ana neman mayar da bara bana, domin kuwa halin da gonakin Kano ke ciki; ya zama abin takaici kwarai da gaske.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

A shekarun baya, ‘yar gayaunar bayan gida kan iya samar da wasu nau’ikan abinci, wadanda suke daukar lokaci ana amfani da su, kama daga kan wake, kayan miya da kuma dawar tuwo, amma yanzu sakamakon yadda birane suke kara mamaye gonaki da kuma yadda dillalan filaye suka samu sabuwar sana’a, ta yadda masu hannu da shuni ke saye maka-makan gonaki tare da mayar da su filaye; ta hanyar daidai kudinka daidai shagalinka.

Har ila yau, karancin gonakin noman abinci; ba karamar barazana ce ga harkar samar da abinci ga al’ummar Jihar Kano ba, musamman idan aka dubi yadda wasu manyan kamfanonin  kasashen waje ke saye ire-iren wadannan gonaki tare da katange su, an hana manoma yin noma; sannan da sunan da aka sayi gonar na cewa za a yi, jama’a su samu aikin yi; shi ma ba a yi ba.

Idan ka bi hanyar Kano zuwa Wudil, Wudil Zuwa Kwanar Garko, haka nan titin Hadeja; takanin Gunduwawa zuwa Jogana, babu wasu sauran gonakin noma, sai manyan katangu da masu kudi suka saye suka killace.

Neja

Dangane da wannan dambarwa, wakilinmu na Jihar Neja ya tattauna da wani mai saye da sayarwa a kan harkar filaye da gidaje, Malam Lawal Yaro; wanda ya bayyana cewa magana ta gaskiya illar sayar da gonaki ya fi alfanunsa yawa.

Domin kuwa a cewar tasa, za ka tarar da iyali guda suna da gonar da ta kai girman hekta sama da hamsin, wanda dukkanin su suka dogara a kanta, amma da zarar wata baraka ta taso a tsakanin su, sai su sayar wa da mutum daya, wanda shi zai noma ba, ba kuma zai ba wa wani ya yi noman ba.

Haka zalika, matsalar tsaro ta hana mutune zuwa dazuka wadanda ke da nisa, wanda kuma in dai har mutum manomi ne na gaskiya, ya fada cikin irin wannan jarabawa; dole ne ya koma makwafta don neman rufin asiri kamar yadda take faruwa a tsakanin Nufawa da Gwarawa a wannan lokaci.

Dalili kuwa shi ne, abin takaici ne ka tashi daga Minna zuwa Bidda ka ga filayen gonaki an killace su ba a yin noman kwata-kwata, kuma ba a ba wa wasu su yi noman ba.

Haka zalika, wannan tsadar abinci da ake fama da ita; ta biyo bayan rashin samun damar noma wadataccen abinci ne tare da sayar da gonakin da ake yi ga ‘yan kasuwa, wasu na yanka filayen suna sayarwa, wasu kuma suna killace su ba tare da yin komai a wurin ba.

Nassarawa

Har ila yau, daga Jihar Nassarawa; wakilinmu ya samu tattaunawa da wasu daga cikin manoma, dangane da alfanu da kuma rashin alfanun mayar da gonaki filaye.

Alhaji Abubakar Danjuma, guda ne daga cikin manoman jihar wanda ya bayyana cewa, a shekarun baya ba a samun matsalar abinci, musamman abin da ya shafi bangaren kayan miya sakamakon cewa akwai wadatattun filaye a kusa da gari.

A wannan lokaci, mutane suna noma abin da za su ci a gida, idan kayan miya ne kuma ga lambu a kusa da gida; sai dai kawai a je a debo a kawo, amma yanzu komai ya yi wahala sakamakon babu lambun noman tumatur ko Alaiyahu da sauran makamantansu. Ya kara da cewa, kamata ya yi idan aka yanka nan ya koma gidaje, sai kuma a bude wani wurin daban.

A bangare guda kuma, Mista Asile Manga ya bayyana nasa ra’ayin, inda ya bayyana cewa; yanzu mutane sun yi yawa a wannan kasa. Saboda haka, wajibi ne kowa ya nemi matsugunin da zai zauna da iyalinsa.

Don haka, dole ne a yanka gonakin da ke kusa da gari, duk da dai kuma bai kamata a rika sare bishiyoyin da ke kusa da su ba. Domin kuwa, barin itace yana da matukar amfani.

Kaduna

Masana harkokin gidaje a Nijeriya, sun bayyana irin karancin matsalar gidaje da ake samu a wannan kasa, wanda yawansu ya kai kimanin miliyan 22; duk da kokarin gwamanatoci ke yi na dukufa wajen mayar da gonaki zuwa gidaje.

Har ila yau, masanan bayyana cewa; kashi 80 cikin 100 na ‘yan Nijeriya, ba sa iya gina gida ko fitar da kudi su saya. Kazalika, matsalar na kara munana da karancin gidaje 900,000 a kowace shekara.

A Jihar Kaduna, mafi yawan gonakin da ake yin noma; yanzu sun fara komawa birane, lamarin da wasu suke ganin akwai alfanun mayar da gonakin zuwa gidaje, wasu kuma ke ganin hakan ba shi da wani alfanu.

A kokarin da ‘yan kasuwa ke ci gaba da yi na mayar da gonaki zuwa filaye a halin yanzu, ya sa Gwamnatin Jihar Kaduna kirkirar sabbin birane; domin fadada birnin Kaduna, ta hanyar mayar da gonaki zuwa gidajen zama.

Mutane da dama na ci gaba da kokawa dangane da yadda ake mamayar gonakinsu ana mayar da su gidaje, koda-yake wasu kuma na ganin yin hakan na da matukar alfanun gaske.

Alhaji Shafi’u Salisu Abubakar, Shugaban Kungiyar Dillalan Gidaje da Filaye ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa, akwai alfanu mai tarin yawan gaske wajen mayar da gonaki birane.

Ya kara da cewa, duk da yadda ake mayar da gonaki gidaje har yanzu ana samun karancin gidajen zama ga al’umma, wanda wannan ba karamar babbar barazana ba ce.

“A nan Jihar Kaduna, idan ka dauki Dan Bushiya da Dan Huni da Keke da dai sauran sabbin wurare, duk sun zama kananan birane; wanda a shekaru goma baya duk daji ne wurin ko da kudi aka ce ka shiga, ba za ka iya shiga ba; amma yanzu wurin ya koma kamar kana Abuja.

Saboda haka, ko shakka babu akwai alfanu mai yawan gaske; idan aka mayar da gonaki zuwa birane. Sannan kuma, ai yin hakan ba zai hana a yi noman ba, domin kuwa har yanzu muna da sauran wuraren yin wannan noma masu yawan gaske a fadin wannan jiha,” in ji shi.

Katsina

Daga Jihar Katsina, wakilinmu ya tattauna tare da jin ta bakin wadanda ke da ruwa da tsaki, kan wannan dambarwa, Alhaji Hassan Tsagem; guda ne daga cikin ‘yan kasuwa masu sayen gonaki suna mayar da su filaye; domin sayarwa jama’a, wanda ya dauki tsawon lokaci yana wannan sana’a.

Har ilayau, Tsagem kara da cewa; amfanin mayar da gonaki filaye na da matukar muhimmanci, musamman a wurinsu ‘yan kasuwa sana’a mai matukar kyau a gare su, na biyu kuma hanya ce ta saukaka wa masu karamin karfi, domin mallakar filaye samakon cewa, a irin wannan lokaci mutane ba za su iya sayen gidaje a mayan unguwanni ko sayen fili awon gwamnati ba.

“A duk yayin da muka sayi gona, wanda dama mafiyawan gonakin a wajen gari suke, sai mu yanka su zuwa filaye tare da sayar da su ga talakawa masu karamin karfi.

Gaskiyar magana shi ne, babu wani mutumin kauye da ke son rabuwa da abin da ya gada iyaye da kakannin, idan har ba ya zama dole ba, domin wani lokacin idan ba ka sayar ba; za a yi maka barazanar kwace wurin, hakan ya sa ake sayarwa don samun kwanciyar hankali, a cewar ta Kalla.

Jigawa

Dangane da sauya gonakin noma zuwa filaye, a Jihar Jigawa ma dai ba ta sauya zani ba, domin kuwa al’ummar jihar kullum na ci gaba da kokawa.

Alhaji Ahmad Rufa’i, manomi ne kuma mazaunin Birnin Dutse, ya bayyana lamarin a matsayin wani babban kalubale, wanda ke jefa dubban matasa cikin wani yanayi na rashin aikin yi tare da zaman kashe wando.

Kazalika ya bayyana cewa, duk da kasancewar mafi yawan gonakin, gwamnati na amfani da su wajen gina ma’aikatu da gidajen ma’aikata, wanda ko shakka babu shi ma wani ci gaba ne, amma hakan na kara barazanar karancin samun abinci.

Shi kuwa a nasa bangaren, wani dillalin filaye mai suna Alhaji Mu’azu, ya bayyana wannan lamari a matsayin ci gaba musamman ga manyan birane a jihar ta Jigawa.

Mu’azu ya kara da cewa, a duk inda ka ga ana sauya gonaki zuwa filaye; babu wani abu a wannan wuri illa ci gaba ga al’ummar da ke zaune a yankin.

“Wadansu gonakin an mayar da su masana’antu, wanda hakan ya bai wa matasa damar samun ayyukan yi tare da bunkasa tattalin arzikinsu. Sannan, dukkanin wani birni; yana bunkasa ne sakamakon amfani da gonakin da ake yi zuwa gine-gine da kuma kawata shi.

Kebbi

Jihar Kebbi, na daya daga cikin Jihohin Nijeriya wadanda suka yi suna wajen noma da samar da abinci, amma a halin yanzu ita ma na fama da matsalar yanka gonaki ana mayar da da su filaye, don gina gidajen kwana.

Ko shakka babu, wannan matsala da ke kunno kai; za ta yi matukar jawo karancin samar da abinci ga jihohin kasar nan, musamman Jihar Kebbi da ta yi kaurin suna wajen noma abinci a fadin Nijeriya baki-daya.

A wata tattaunawa da wakilinmu ya yi da wani tsohon ma’aikacin ma’aikatar filaye da gina gidaje, wanda ya nemi a sakaye sunansa ya bayyana cewa, “Matsalar mayar da gonaki filaye don gina gidaje, ba karamar matsala ba ce; domin kuwa za a kai ga lokacin da ba za a iya samar da abinci a jihohinmu na Nijeriya ba. Don haka, ya zama wajibi ga gwamnatotin jihohi da  tarayya su farga don samar da mafita.

Shi ma wani manomi mai suna Audu Bello Birnin Kebbi ya bayyyana cewa, a shekaru goma da suka gabata yana da gonakin noman abinci dai-dai har guda tara wadanda ya gada daga wurin mahaifinsa, amma sakamakon wannan matsala ta mayar da gonaki zuwa filaye, ta sa ya rabu da guda takwas saura daya kacal a halin yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Tona Asirin Kungiyoyin Addinin Da Ke Daukar Nauyin Ta’addanci

Next Post

Matsayar Sin Game Da Burin Wanzar Da Zaman Lafiya A Duniya

Related

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

47 minutes ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

15 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

18 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

24 hours ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

1 day ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

2 days ago
Next Post
Matsayar Sin Game Da Burin Wanzar Da Zaman Lafiya A Duniya

Matsayar Sin Game Da Burin Wanzar Da Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.