ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci

by Sani Anwar, Abdullahi Muh'd Sheka and Muhammad Awwal Umar and 5 more
3 years ago
Gonaki

Wata matsala da ke kunno kai tare da yin barazana ga harkokin noma a halin yanzu ita ce, batun mayar da gonaki zuwa filaye ko gidajen kwana a kafatanin jihohin Arewacin wannan kasa baki-daya.

Har ila yau, wannan dalili ne ya sa wakilanmu daga wasu jihohi na Arewacin kasar, suka tattara mana rahotanni ta hanyar tattaunawa da wadanda abin ya shafa, domin kokarin lalubo bakin zaren; ta hanyar jin alfanu da kuma rashin alfanu na wannan dambarwa, inda wasu suka goyi bayan mayar da filayen gonaki, wasu kuma suka soki yin hakan.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka

Ga dai rahotannin da wakilan namu suka aiko mana da su:

ADVERTISEMENT

Kano

Batun sayar da gonakin noman abinci, musamman ga masu karamin karfin da suke noma dan wani abu daga cikin abincin da suke amfani da shi a gidajensu, yanzu haka ana iya cewa; ana neman mayar da bara bana, domin kuwa halin da gonakin Kano ke ciki; ya zama abin takaici kwarai da gaske.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A shekarun baya, ‘yar gayaunar bayan gida kan iya samar da wasu nau’ikan abinci, wadanda suke daukar lokaci ana amfani da su, kama daga kan wake, kayan miya da kuma dawar tuwo, amma yanzu sakamakon yadda birane suke kara mamaye gonaki da kuma yadda dillalan filaye suka samu sabuwar sana’a, ta yadda masu hannu da shuni ke saye maka-makan gonaki tare da mayar da su filaye; ta hanyar daidai kudinka daidai shagalinka.

Har ila yau, karancin gonakin noman abinci; ba karamar barazana ce ga harkar samar da abinci ga al’ummar Jihar Kano ba, musamman idan aka dubi yadda wasu manyan kamfanonin  kasashen waje ke saye ire-iren wadannan gonaki tare da katange su, an hana manoma yin noma; sannan da sunan da aka sayi gonar na cewa za a yi, jama’a su samu aikin yi; shi ma ba a yi ba.

Idan ka bi hanyar Kano zuwa Wudil, Wudil Zuwa Kwanar Garko, haka nan titin Hadeja; takanin Gunduwawa zuwa Jogana, babu wasu sauran gonakin noma, sai manyan katangu da masu kudi suka saye suka killace.

Neja

Dangane da wannan dambarwa, wakilinmu na Jihar Neja ya tattauna da wani mai saye da sayarwa a kan harkar filaye da gidaje, Malam Lawal Yaro; wanda ya bayyana cewa magana ta gaskiya illar sayar da gonaki ya fi alfanunsa yawa.

Domin kuwa a cewar tasa, za ka tarar da iyali guda suna da gonar da ta kai girman hekta sama da hamsin, wanda dukkanin su suka dogara a kanta, amma da zarar wata baraka ta taso a tsakanin su, sai su sayar wa da mutum daya, wanda shi zai noma ba, ba kuma zai ba wa wani ya yi noman ba.

Haka zalika, matsalar tsaro ta hana mutune zuwa dazuka wadanda ke da nisa, wanda kuma in dai har mutum manomi ne na gaskiya, ya fada cikin irin wannan jarabawa; dole ne ya koma makwafta don neman rufin asiri kamar yadda take faruwa a tsakanin Nufawa da Gwarawa a wannan lokaci.

Dalili kuwa shi ne, abin takaici ne ka tashi daga Minna zuwa Bidda ka ga filayen gonaki an killace su ba a yin noman kwata-kwata, kuma ba a ba wa wasu su yi noman ba.

Haka zalika, wannan tsadar abinci da ake fama da ita; ta biyo bayan rashin samun damar noma wadataccen abinci ne tare da sayar da gonakin da ake yi ga ‘yan kasuwa, wasu na yanka filayen suna sayarwa, wasu kuma suna killace su ba tare da yin komai a wurin ba.

Nassarawa

Har ila yau, daga Jihar Nassarawa; wakilinmu ya samu tattaunawa da wasu daga cikin manoma, dangane da alfanu da kuma rashin alfanun mayar da gonaki filaye.

Alhaji Abubakar Danjuma, guda ne daga cikin manoman jihar wanda ya bayyana cewa, a shekarun baya ba a samun matsalar abinci, musamman abin da ya shafi bangaren kayan miya sakamakon cewa akwai wadatattun filaye a kusa da gari.

A wannan lokaci, mutane suna noma abin da za su ci a gida, idan kayan miya ne kuma ga lambu a kusa da gida; sai dai kawai a je a debo a kawo, amma yanzu komai ya yi wahala sakamakon babu lambun noman tumatur ko Alaiyahu da sauran makamantansu. Ya kara da cewa, kamata ya yi idan aka yanka nan ya koma gidaje, sai kuma a bude wani wurin daban.

A bangare guda kuma, Mista Asile Manga ya bayyana nasa ra’ayin, inda ya bayyana cewa; yanzu mutane sun yi yawa a wannan kasa. Saboda haka, wajibi ne kowa ya nemi matsugunin da zai zauna da iyalinsa.

Don haka, dole ne a yanka gonakin da ke kusa da gari, duk da dai kuma bai kamata a rika sare bishiyoyin da ke kusa da su ba. Domin kuwa, barin itace yana da matukar amfani.

Kaduna

Masana harkokin gidaje a Nijeriya, sun bayyana irin karancin matsalar gidaje da ake samu a wannan kasa, wanda yawansu ya kai kimanin miliyan 22; duk da kokarin gwamanatoci ke yi na dukufa wajen mayar da gonaki zuwa gidaje.

Har ila yau, masanan bayyana cewa; kashi 80 cikin 100 na ‘yan Nijeriya, ba sa iya gina gida ko fitar da kudi su saya. Kazalika, matsalar na kara munana da karancin gidaje 900,000 a kowace shekara.

A Jihar Kaduna, mafi yawan gonakin da ake yin noma; yanzu sun fara komawa birane, lamarin da wasu suke ganin akwai alfanun mayar da gonakin zuwa gidaje, wasu kuma ke ganin hakan ba shi da wani alfanu.

A kokarin da ‘yan kasuwa ke ci gaba da yi na mayar da gonaki zuwa filaye a halin yanzu, ya sa Gwamnatin Jihar Kaduna kirkirar sabbin birane; domin fadada birnin Kaduna, ta hanyar mayar da gonaki zuwa gidajen zama.

Mutane da dama na ci gaba da kokawa dangane da yadda ake mamayar gonakinsu ana mayar da su gidaje, koda-yake wasu kuma na ganin yin hakan na da matukar alfanun gaske.

Alhaji Shafi’u Salisu Abubakar, Shugaban Kungiyar Dillalan Gidaje da Filaye ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa, akwai alfanu mai tarin yawan gaske wajen mayar da gonaki birane.

Ya kara da cewa, duk da yadda ake mayar da gonaki gidaje har yanzu ana samun karancin gidajen zama ga al’umma, wanda wannan ba karamar babbar barazana ba ce.

“A nan Jihar Kaduna, idan ka dauki Dan Bushiya da Dan Huni da Keke da dai sauran sabbin wurare, duk sun zama kananan birane; wanda a shekaru goma baya duk daji ne wurin ko da kudi aka ce ka shiga, ba za ka iya shiga ba; amma yanzu wurin ya koma kamar kana Abuja.

Saboda haka, ko shakka babu akwai alfanu mai yawan gaske; idan aka mayar da gonaki zuwa birane. Sannan kuma, ai yin hakan ba zai hana a yi noman ba, domin kuwa har yanzu muna da sauran wuraren yin wannan noma masu yawan gaske a fadin wannan jiha,” in ji shi.

Katsina

Daga Jihar Katsina, wakilinmu ya tattauna tare da jin ta bakin wadanda ke da ruwa da tsaki, kan wannan dambarwa, Alhaji Hassan Tsagem; guda ne daga cikin ‘yan kasuwa masu sayen gonaki suna mayar da su filaye; domin sayarwa jama’a, wanda ya dauki tsawon lokaci yana wannan sana’a.

Har ilayau, Tsagem kara da cewa; amfanin mayar da gonaki filaye na da matukar muhimmanci, musamman a wurinsu ‘yan kasuwa sana’a mai matukar kyau a gare su, na biyu kuma hanya ce ta saukaka wa masu karamin karfi, domin mallakar filaye samakon cewa, a irin wannan lokaci mutane ba za su iya sayen gidaje a mayan unguwanni ko sayen fili awon gwamnati ba.

“A duk yayin da muka sayi gona, wanda dama mafiyawan gonakin a wajen gari suke, sai mu yanka su zuwa filaye tare da sayar da su ga talakawa masu karamin karfi.

Gaskiyar magana shi ne, babu wani mutumin kauye da ke son rabuwa da abin da ya gada iyaye da kakannin, idan har ba ya zama dole ba, domin wani lokacin idan ba ka sayar ba; za a yi maka barazanar kwace wurin, hakan ya sa ake sayarwa don samun kwanciyar hankali, a cewar ta Kalla.

Jigawa

Dangane da sauya gonakin noma zuwa filaye, a Jihar Jigawa ma dai ba ta sauya zani ba, domin kuwa al’ummar jihar kullum na ci gaba da kokawa.

Alhaji Ahmad Rufa’i, manomi ne kuma mazaunin Birnin Dutse, ya bayyana lamarin a matsayin wani babban kalubale, wanda ke jefa dubban matasa cikin wani yanayi na rashin aikin yi tare da zaman kashe wando.

Kazalika ya bayyana cewa, duk da kasancewar mafi yawan gonakin, gwamnati na amfani da su wajen gina ma’aikatu da gidajen ma’aikata, wanda ko shakka babu shi ma wani ci gaba ne, amma hakan na kara barazanar karancin samun abinci.

Shi kuwa a nasa bangaren, wani dillalin filaye mai suna Alhaji Mu’azu, ya bayyana wannan lamari a matsayin ci gaba musamman ga manyan birane a jihar ta Jigawa.

Mu’azu ya kara da cewa, a duk inda ka ga ana sauya gonaki zuwa filaye; babu wani abu a wannan wuri illa ci gaba ga al’ummar da ke zaune a yankin.

“Wadansu gonakin an mayar da su masana’antu, wanda hakan ya bai wa matasa damar samun ayyukan yi tare da bunkasa tattalin arzikinsu. Sannan, dukkanin wani birni; yana bunkasa ne sakamakon amfani da gonakin da ake yi zuwa gine-gine da kuma kawata shi.

Kebbi

Jihar Kebbi, na daya daga cikin Jihohin Nijeriya wadanda suka yi suna wajen noma da samar da abinci, amma a halin yanzu ita ma na fama da matsalar yanka gonaki ana mayar da da su filaye, don gina gidajen kwana.

Ko shakka babu, wannan matsala da ke kunno kai; za ta yi matukar jawo karancin samar da abinci ga jihohin kasar nan, musamman Jihar Kebbi da ta yi kaurin suna wajen noma abinci a fadin Nijeriya baki-daya.

A wata tattaunawa da wakilinmu ya yi da wani tsohon ma’aikacin ma’aikatar filaye da gina gidaje, wanda ya nemi a sakaye sunansa ya bayyana cewa, “Matsalar mayar da gonaki filaye don gina gidaje, ba karamar matsala ba ce; domin kuwa za a kai ga lokacin da ba za a iya samar da abinci a jihohinmu na Nijeriya ba. Don haka, ya zama wajibi ga gwamnatotin jihohi da  tarayya su farga don samar da mafita.

Shi ma wani manomi mai suna Audu Bello Birnin Kebbi ya bayyyana cewa, a shekaru goma da suka gabata yana da gonakin noman abinci dai-dai har guda tara wadanda ya gada daga wurin mahaifinsa, amma sakamakon wannan matsala ta mayar da gonaki zuwa filaye, ta sa ya rabu da guda takwas saura daya kacal a halin yanzu.

Gonaki
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Gonaki
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Gonaki
Muhammad Awwal Umar
+ posts Bio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Kwana 100 A Karagar Mulki: Kamun Ludayin Sabbin Gwamnoni
Gonaki
Zubairu M Lawal
+ posts Bio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    2027: Miyetti Allah Ta Yi Barazanar Ƙauracewa APC Kan Ci Gaba da Tsare Boɗejo
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tsaftar Muhalli: Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kasuwar Tumatir A Lafia
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Samar Da Abinci Mai Gina Jiki: Gwamna Sule Ya Duba Gonakin Shinkafa A Jangwa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda Ya Tallafawa Manoma Da Kayan Aikin Gona Na Miliyoyin Naira A Nasarawa
Gonaki
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Uba Sani Ya Yi Jimamin Rasuwar Dan Jarida Jafaru Yakubu Maitama
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Fara Rabon Takin Zamani Kyauta Ga Manoma 150,000
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zaka Iya Sayar da Takin Gwamnati Ka Sayawa Iyalinka Kaji — Imam Nuradden
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tsaro: ACI Zata Kira Taron Gaggawa Na Masu Ruwa Da Tsaki A Kaduna
Gonaki
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda
Gonaki
Munkaila T. Abdullahi
+ posts Bio
  • Munkaila T. Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/munkaila-t-abdullahi/
    Matsalar Tsaro Da Hadurran Kwalekwale Da Ambaliyar Ruwa Na Cin Rayuka A Arewa
  • Munkaila T. Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/munkaila-t-abdullahi/
    NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno
  • Munkaila T. Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/munkaila-t-abdullahi/
    Namadi Ya Lashe Zaben Gwamna A Jigawa
  • Munkaila T. Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/munkaila-t-abdullahi/
    Manoman Alkama 200 Za Su Amfana Da Shirin NALDA A Jihar Jigawa
Gonaki
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Matsayar Sin Game Da Burin Wanzar Da Zaman Lafiya A Duniya

Matsayar Sin Game Da Burin Wanzar Da Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.