• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Minista Ya Kaddamar Da Ginin Radio House Da Aka Yi Wa Kwaskwarima A Abuja

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Yadda Minista Ya Kaddamar Da Ginin Radio House Da Aka Yi Wa Kwaskwarima A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da ginin Radio House da aka gyara a Abuja, wanda ke nuna wani babban mataki na dawo da muhimman ababen more rayuwa da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.

 

Da yake zagaye don duba ginin mai hawa 14, ministan ya bayyana halin lalacewar da ginin ya shiga har tsawon kusan shekaru 20.

  • Kotu Ta Sake Bayar Da Belin Tsohon Gwamnan Kogi Kan Naira Miliyan 500
  • Tallafin Wutar Lantarki Ya Kai Naira Biliyan 199.64 A Nijeriya – NERC

Ya ce: “Lokacin da na zo nan, wurin nan ya lalace— na’urorin esi ba sa aiki, lif na hawa ba ya aiki, kuma ma’aikata na hawa har hawa tara ko goma don isa ofisoshin su. Hatta banɗakuna sun lalace; wannan bai dace ba.”

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Ministan ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa gaggawar amincewar da ya yi na kuɗaɗen da suka ba da damar gyaran ginin, wanda ke ɗauke da ma’aikatar da kuma Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya.

 

“Bisa taimakon Shugaban Ƙasa, mun mayar da wannan ginin ya zama wurin aiki mai amfani kuma mai inganci, na’urorin esi suna aiki, dukkan lif suna aiki, kuma kayan aikin sun zama na zamani. A karo na farko cikin kusan shekaru ashirin, Radio House ya dawo aiki, kuma ma’aikata suna farin ciki.”

 

A cewar Dakta Suleiman Haruna, Daraktan Hulɗa da Jama’a da Tsare-tsare, wannan aikin ya dace da burin Shugaba Tinubu na zamanantar da ababen more rayuwa na aikin yaɗa labarai a duk faɗin ƙasar nan.

 

Ministan ya jaddada cewa ana ci gaba da ƙoƙarin yin irin wannan gyaran a tashoshin Rediyon Tarayya na Nijeriya (FRCN) da Gidan Talabijin na Nijeriya (NTA) da ke Kaduna, Legas, da Inugu.

 

Ya ce: “Muna dawo da darajar kadarorin yaɗa labarai na Nijeriya kamar yadda suke a da. Wannan ba kawai gyaran gine-gine ba ne; yana nufin mayar da masana’antar kafofin watsa labarai na Nijeriya ta dace da mafi kyawun masana’antu a duniya.”

 

Ministan ya kuma yi kira ga ma’aikatan da su yi amfani da wannan tagomashin da gwamnati ta bayar ta hanyar yin aiki da ƙwazo da ƙwarewa.

 

Ya ƙara da cewa, “Yanzu da ake ba mu abubuwa masu yawa, dole ne mu ma mu mayar da martani ta hanyar tallafa wa burin Shugaban Ƙasa na farfaɗo da martabar Nijeriya.”

 

Ya jaddada muhimmancin ƙwararrun ‘yan jarida wajen bunƙasar ƙasa, tare da alƙawarin kare yanayin aiki mai kyau, wanda ya haɗa da samar da tsarin albashi da ya dace da matsayin su.

 

Idris ya ce: “Shugaban Ƙasa yana ƙoƙarin yin duk mai yiwuwa don kula da dukkan ɓangarori, amma saboda rawar da kafofin watsa labarai suke takawa da kuma haɗarin da ke tattare da aikin, muna fatan ganin ‘yan jarida suna samun tsarin albashi da ya dace da irin aikin da suke yi wa ƙasar mu.”

 

A nata ɓangaren, Shugabar Kwamitin Haɗin Gwiwa na Ma’aikata a ma’aikatar, Kwamared Chika Ukachukwu, ta yaba da aikin gyaran da aka yi, tana mai cewa kyakkyawan yanayin aiki da aka yi zai ƙarfafa wa ma’aikata gwiwa.

 

Ta kuma miƙa kyautar Gwarzon Jagoranci ga ministan a matsayin yabo bisa jajircewar sa da sadaukarwar sa wajen cimma burin ma’aikatar.

 

Taron ya samu halartar Muƙaddashin Babbar Sakataren Ma’aikatar, Comfort Ajiboye, da Darakta Janar na FRCN, Alhaji Muhammad Bulama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Gwamnatin Yankin Macao

Next Post

Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

Related

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

3 minutes ago
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
Labarai

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

1 hour ago
Kawayen amarya
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

4 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

6 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

8 hours ago
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

17 hours ago
Next Post
Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.