• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Minista Ya Kaddamar Da Ginin Radio House Da Aka Yi Wa Kwaskwarima A Abuja

by Sulaiman
10 months ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da ginin Radio House da aka gyara a Abuja, wanda ke nuna wani babban mataki na dawo da muhimman ababen more rayuwa da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.

 

Da yake zagaye don duba ginin mai hawa 14, ministan ya bayyana halin lalacewar da ginin ya shiga har tsawon kusan shekaru 20.

  • Kotu Ta Sake Bayar Da Belin Tsohon Gwamnan Kogi Kan Naira Miliyan 500
  • Tallafin Wutar Lantarki Ya Kai Naira Biliyan 199.64 A Nijeriya – NERC

Ya ce: “Lokacin da na zo nan, wurin nan ya lalace— na’urorin esi ba sa aiki, lif na hawa ba ya aiki, kuma ma’aikata na hawa har hawa tara ko goma don isa ofisoshin su. Hatta banɗakuna sun lalace; wannan bai dace ba.”

 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

Ministan ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa gaggawar amincewar da ya yi na kuɗaɗen da suka ba da damar gyaran ginin, wanda ke ɗauke da ma’aikatar da kuma Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya.

 

“Bisa taimakon Shugaban Ƙasa, mun mayar da wannan ginin ya zama wurin aiki mai amfani kuma mai inganci, na’urorin esi suna aiki, dukkan lif suna aiki, kuma kayan aikin sun zama na zamani. A karo na farko cikin kusan shekaru ashirin, Radio House ya dawo aiki, kuma ma’aikata suna farin ciki.”

 

A cewar Dakta Suleiman Haruna, Daraktan Hulɗa da Jama’a da Tsare-tsare, wannan aikin ya dace da burin Shugaba Tinubu na zamanantar da ababen more rayuwa na aikin yaɗa labarai a duk faɗin ƙasar nan.

 

Ministan ya jaddada cewa ana ci gaba da ƙoƙarin yin irin wannan gyaran a tashoshin Rediyon Tarayya na Nijeriya (FRCN) da Gidan Talabijin na Nijeriya (NTA) da ke Kaduna, Legas, da Inugu.

 

Ya ce: “Muna dawo da darajar kadarorin yaɗa labarai na Nijeriya kamar yadda suke a da. Wannan ba kawai gyaran gine-gine ba ne; yana nufin mayar da masana’antar kafofin watsa labarai na Nijeriya ta dace da mafi kyawun masana’antu a duniya.”

 

Ministan ya kuma yi kira ga ma’aikatan da su yi amfani da wannan tagomashin da gwamnati ta bayar ta hanyar yin aiki da ƙwazo da ƙwarewa.

 

Ya ƙara da cewa, “Yanzu da ake ba mu abubuwa masu yawa, dole ne mu ma mu mayar da martani ta hanyar tallafa wa burin Shugaban Ƙasa na farfaɗo da martabar Nijeriya.”

 

Ya jaddada muhimmancin ƙwararrun ‘yan jarida wajen bunƙasar ƙasa, tare da alƙawarin kare yanayin aiki mai kyau, wanda ya haɗa da samar da tsarin albashi da ya dace da matsayin su.

 

Idris ya ce: “Shugaban Ƙasa yana ƙoƙarin yin duk mai yiwuwa don kula da dukkan ɓangarori, amma saboda rawar da kafofin watsa labarai suke takawa da kuma haɗarin da ke tattare da aikin, muna fatan ganin ‘yan jarida suna samun tsarin albashi da ya dace da irin aikin da suke yi wa ƙasar mu.”

 

A nata ɓangaren, Shugabar Kwamitin Haɗin Gwiwa na Ma’aikata a ma’aikatar, Kwamared Chika Ukachukwu, ta yaba da aikin gyaran da aka yi, tana mai cewa kyakkyawan yanayin aiki da aka yi zai ƙarfafa wa ma’aikata gwiwa.

 

Ta kuma miƙa kyautar Gwarzon Jagoranci ga ministan a matsayin yabo bisa jajircewar sa da sadaukarwar sa wajen cimma burin ma’aikatar.

 

Taron ya samu halartar Muƙaddashin Babbar Sakataren Ma’aikatar, Comfort Ajiboye, da Darakta Janar na FRCN, Alhaji Muhammad Bulama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano
Manyan Labarai

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Next Post
Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

LABARAI MASU NASABA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.