ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
Ilimi

Kamar kowane mako shafin TASKIRA ya kan zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, ciki sun hadar da; zamatakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu. Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da abin da ya shafi ilimi, inda shafin TASKIRA ya ji ta bakin wasu daga cikin mabiya shafin game da wannan batu; Ta wacce hanya rashin ilimi yake cutar da al’umma bakidaya?, wacce hanya ya kamata a bi wajen kara habaka hanyar samun ilimi?, ko ta wacce hanya kimiya da fasaha ke taka rawa wajen samar da ilimi?, fadi amfanin ilimi”. Ga dai bayanan nasu kamar haka:

Sunana Naja’atu Baffa Jihar Kaduna:

Ilimi

ADVERTISEMENT

Rashin Ilimi na cutar da al’umma ta hanyoyi da dama kamar; hana samun kwakkwaran aiki na dogaro da kai da kuma aikin samun kudi, idan da babu ilimi da mutane na ta gwagwarmaya me wahala. Hanyoyin habaka ilimi su ne; samun kimiyya da fasaha mai kyau, sannan a sako iyaye cikin al’amuran da suka shafi ilimin. Kimiya da fasaha na taka rawa sosai a wajen ilimi kamar yanar gizo-gizo a yanzu na taimakawa dalibai dsn samun saukin karatu ba tare da sun sha wata wahala ba, sannan yana taimakawa malamai wajen tsara aikin su na tsare-tsaren makaranta cikin sauki, yana kuma taimakawa wajen sadarwa tsakanin malamai, dalibai da ma iyaye bakidaya ta hanya mai sauki. Ilimi yana da amfanoni da yawa kamar; ilimi na kara zurfin tunani a gurin dan’adam musamman wajen warware matsaloli, sai kuma hanyar samun kudi ne cikin sauki, ilimi na taimakawa wajen samun ilimi don a matsayinka na mutum mai zurfin tunani zai iya yu wa kasan illolin wadansu abincincika da suke da hatsari ga dan’adam, ilimi ka iya raya al’adar mutane har ma da karbar wadansu al’adun na mabambantan mutane. Shawarar da zan bawa iyayen da ba sa tura ‘ya’yansu makaranta ita ce; ta hanyar tura yara makaranta hakan zai ba su damar cikar burikansu, kiwon lafiyarsu har ma da iyayen, amfani da baiwar da Allah ya basu, sannan yaran da ba a tura su makaranta ba sun fi fadawa tarkon talauci zuwa bin abokan banza na unguwa.

Sunana Abba Abubakar Yakubu, Daga Jos A Jihar Filato:

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

Ilimi

Ilimi Gishirin Rayuwa

Babu shakka ba tun yanzu ba, dan’adam ya dade da fahimtar muhimmancin ilimi ga cigaban rayuwarsa. Walau ilimin addini ko na cigaban rayuwa. Addinin Musulunci ya koyar da mu muhimmancin bai wa ilimi fifiko, kamar yadda aka rawaito a cikin Hadisi. Ma’aikin Allah (SAWA) yana cewa ‘mu nemi ilimi ko da a Birnin Sin ne’. Kuma ya gaya mana cewa, “haddar yaro karami kamar rubutu ne akan dutse…” Kenan, wannan yana karfafa mana gwiwa mu koyawa yaranmu Ilimi tun suna kanana, don za su fi rikewa ya zauna a kwakwalensu. Ilimi tamkar fitila take, yana haskakawa mutum abubuwa na rayuwa, yadda zai koyi zaman duniya da gina wa kansa rayuwa mai inganci. Wannan ilimin kuwa ko da wanda ake koya a wajen aiki ne ko wajen sana’a, ba lallai sai a cikin aji ba. Ana koyon ilimi na aiki da hannu, ko da baki ko a rubuce. Sannan yanzu da zamani ya canza, akwai kafofin sadarwa daban-daban da mutum zai iya samun ilimi ba tare da ya shiga aji ba. Akwai manhajoji irin su YouTube, LinkedIn, Facebook da sauransu da mutum zai iya shiga ya koyi abubuwa da dama na ilimi. Lallai yana da kyau iyaye su rika zaunar da yaran su suna koya musu karatu da ilimin rayuwa, tun daga matakin gida, ko a dauki nauyin mai koya musu, ko kuma a saka su a makaranta. Rashin sa yaro a makaranta na sa ya girma babu wayo, kuma zai rika rayuwar jahilci, da rashin sanin inda yake masa ciwo. Sannan gwamnati ta saukaka hanyoyin samun ilimi, a rika koyarwa da harshen uwa a matakin farko, a samar da ilimi kyau, a rika ba da tallafin karatu ga manya.

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

Ilimi

To magana ta gaskiya hanyoyin da rashin ilimi ke cutar da al’umma suna da yawa domin shi ilimi jigo ne na rayuwar dan’adam muddun kuwa aka ce babu shi to dole abubuwa da dama ba za su tafi daidai ba, domin shi ilimi dan jagora ne ga duk kanin dan’adam shi ke haskawa mutum hanyar daya kamata ya bi da wacce ya kamata ya kaucewa don matsalolin da rashin ilimi ke haifarwa sun fi gaban kidayawa ko kirdado. To magana ta gaskiya a wannan fannin gwamnati ya kamata ta tashi tsaye wajen inganta fannin ilimin dama samar da shi kyauta ga duk kanin al’ummar kasa, sai kuma iyaye suma su tashi tsaye wajen kulawa da sa ‘ya’yansu a makaranta da kuma kula da zuwan yaran akan lokaci. To magana ta gaskiya kimiyya da fasaha tana bada gagarumar gudunmawa wajen saukaka samun ilimi a wannan zamani da muke ciki shi ya sa za ka ga dukkanin kasashen da suka cigaba ta fannin ilimin kimiyya da fasaha to sun fi samun cigaba a fannin ilimi. To amfanin ilimi ko muhimmancin ilimi ga rayuwar dan’adam ya fi gaban kidayawa ko kirdado domin sai da ilimi ne rayuwar take yin kyau kuma sai da ilimi ne ake samun cigaba a rayuwa. To hakika ya kamata irin wannan iyaye su sake tunani domin fa ilimi shi ne hasken rayuwa wanda duk ya rasa ilimi to ya rasa komai a rayuwarsa don haka ya kamata iyaye su tashi tsaye wajen kulawa da ilimin ‘ya’yansu.

Sunana Fatima Nura Kila A Jihar Jigawa:

Ilimi

Rashin ilimi na haifar da matsaloli musamman a cikin al’umma kamar su sata, fyade, rashin girmama manya duk wadannan rashin ilimi na kawo su. Hanyar daya kamata abi shi ne; Gwamnati ta zage damtse wajen tura yara makarantu da kuma saukaka karatu tun daga matakin firamare, har gaba da sakandare. Ilimin kimiyyya nada matukar amfani ga al’umma ta fuskar tabbatar da sauye-sauye tare da samar da cigaban rayuwa, musamman abin da ya shafi bunkasa tunanin dan’adam wannnan ba karamar taka muhimmiyar rawa yake ba. Ilimi jigo ne sannnan mahadin rayuwa ne, ilimi na da amfani musamman wajen zamantakewa da kuma kasuwancinmu na yau da kullum. Shawarar da zan basu shi ne su bar ‘ya’yansu su je makaranta domin Ilimi shi ne ginshikin rayuwa, mutum mai ilimi ma ya fita daban a cikin al’umma.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Jihar Kano Rano LGA:

Ilimi
Lawan Isma’il

Hanyoyin suna da yawa amma daya daga ciki ita ce; aikata ibada ba daidai ba da sabawa Allah kai tsaye. Samar da ilmi ta internet duk da mafiya yawan wasu mutanen tuni sun yi nisa ta wannan fannin. Wajen kirkirar wasu abubuwan da bamu saba ganinsu ba a yankunanmu. Daya daga cikin amfani Ilmi shi ne; aiki da shi a dukkan al’amuranka. Shawarata a garesu ita ce gaskiya su canja tunani kada iyaye su ga wai yanzu idan ka yi karatu ba a samun aikin yi a’a shi ilmi koda irin ‘yan iskan gari ne za ka ga sun bambanta da wadanda ba su yi ba, a saka yara su yi Ilmi ko wanne iri ne domin a can gaba za a ga amfaninsa. Allah ya sa mudace.

Sunana Aisha T Bello Jihar Kaduna:

Ilimi

Rashin ilimi cuta ce gaskiya, saboda ilimi shi ne kishin zaman duniya, yanzu misali; gida babu miji ya rasu in mata na da ilimi za ta nemi aiki dan ta kula da yaranta. Saboda yanzu duniya da zaran ba maigida ba masu kulawa da marayu Allah ne gatansu. Kimiya da fasaha na taka rawa sosai wajen kawo, cigaba ga al’umma bakidaya. Ga iyayen da basu tura yara makaranta gaskiya babbar cutarwa ce, domin kuwa yanzu duniya ta ci gaba, yanzu idan baka da ilimi kana ji kana gani ka zama dan kallo, don haka iyaye su daure su tura yara makaranta don cigaban al’umma bakidaya. Allah ya amfanar damu baki daya.

Ilimi
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A

MASU ALAKA

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
Taskira

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure
Taskira

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

June 6, 2026
Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
Taskira

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki

May 29, 2026
Next Post
Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana'antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

LABARAI MASU NASABA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026
Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

June 17, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

June 17, 2026
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Ceto Manoma 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Sakkwato, Sun Ƙwato Babura

June 17, 2026
Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola

Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola

June 17, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Shirin Sanya Haraji A Kan Man Fetur Da Kiran Waya

Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Shirin Sanya Haraji A Kan Man Fetur Da Kiran Waya

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.