ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi

by Rabi'at Sidi Bala and Sulaiman
9 months ago
Kishi

Shafi TASKIRA shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban, wadanda suka shafi al’umma. Ciki sun hada da zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu.

 

Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da abin da ya shafi mata masu tsananin kishi, wadanda suke iya halaka kansu saboda kishin da namiji ko abin duniya da kyale-kyale. Wanda dalilin hakan ya sa wannan shafi jin ta bakin wasu daga cikin mabiya shafin game da wannan batu; “Ko me yake janyo hakan?, Ya makomar me aikata hakan yake kasancewa a zamantakewar aure, ko ta rayuwar yau da kullum?, Shin mene ne kishi?, kuma ta wacce hanya ya kamata su bi domin magance matsalolin kishi a yayin da za a karo musu abokiyar zama?”.

ADVERTISEMENT

Ga dai bayanan nasu kamar haka:

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano A Jihar Kano:

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

Kishi halak ne kuma so ne yake kawo kishin. Masu irin wannan kishin karshensu nadama ce. Kishi wani abu ne da ake jinsa a cikin rai, kuma kishi ba sai akan aure ake yin sa ba.Hanyoyin da ya kamata abi wajen magance irin wannan shi ne; muna tuna komai yayi farko to yana da karshe, sannan ba kanta farau ba kuma ba kanta karau ba. Muna saka hakuri da tawakkali mu yi kiyayya ba mai zurfi ba, sannan mu yi soyayya ba mai zurfi ba, a karshe sai abin ya zo mana da sauki. Allah ya sa mu dace, amin.

 

Sunana Comr, Nr. Ibrahim Lawan Stk:

Abubuwa da dama na haifar da kishi amma mafi lura shi ne rashin godiya a wajen Allah subahanahu wata’ala da kuma son zuciya tare da son rai irin na mata. Kishi shi ne son kasancewa da namiji a matsayin abokin tarayya ko zamantakewar Aure ba tare da wata ta ji ra’ayin hakan ba ko kuma ta nuna bukata tare da ra’ayin akan namijin da wata ke rayuwa da shi ba. Hanyoyin da za a bi domin magance matsalolin kishi musamman a lokacin da miji zai karo abokiyar zama sun hada da hakuri, danne zuciya, tare da juriya hadi da biyayya ga duk wani umarni daga wajen miji don kuma kaucewa sabawa umarnin Allah da Manzon sa (S.A.W).

 

Sunana Nabila Dikko, Argungun Jihar Kebbi:

To mafi akasarin dalilai da ke sa mata irin wannan kishi shi ne; karancin fahimta da rashin hakuri, da son mallaki namiji su kadai, da son zuciya, kuma hakan na kawo rashin zaman lafiya da rikici da lalacewar dangantaka. Kishi wani abu ne da ke sa zuciya ta dinga son mallakar wani abu ita kadai ko abin da kake da shi ko tsoron rasa shi. A musulinci, kishi halas ne idan bai kauce wa ka’ida ba. Domin magance kishi dole sai mace ta dogara ga addu’a, ta daidaita tunaninta, ta rungumi gaskiyar cewa mijinta yana iya kara aure, sannan ta mayar da hankali wajen kyautatawa maigidanta ba tare da yin abubuwan da ba su dace ba. Shawarata ga mata su kasance masu natsuwa, su guji haddasa rigima. Sai maza ku kasance masu adalci, ku bayyana gaskiya, ku kiyaye hakkin kowace mata, a daidaita adalci ku daina haddasa tsananin kishi a tsakanin matanku.

 

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To, da farko dai akwai jahilci domin shi ke jawo mutum ya kashe kan sa, don indai mutum yana da ilimi ya san illar kashe kai. Sai na biyu kuma rashin rungumar kaddarar da Allah ya kaddarawa mutum domin ita kaddara bata canjawa. To, kishi wani abu ne da Allah yake halittar mutane da shi maza da mata to a lokuta da dama maza su kan yi kokari wajen sarrafa nasu sabanin wasu daga cikin mata da kishin yake sa su aikata aikin da-na-sani ko ma su hallaka kan su.

 

Sunana Hafsat Sa’eed, daga Neja:

Kishi yana cikin addinin musulunci amma kuma akwai kishin hauka irin wanda mace za ta je ta hallaka ‘yar’uwarta ko abin da ‘yar’uwarta ta yi sai ta yi. Mutum yana da wahala ya daukowa kansa babban aiki. Idan namiji zai karo aure ya kamata ka bashi goyan baya, ka yi masa fatan alkhairi, haka idan ta shigo ka samu ku zauna lafiya dole akwai abin da zai sa ka yi kishi sai ka yi daidai misali ba wanda ya haura ka’ida ba.

 

Sunana Hassana Yahaya Iyayi, daga Jihar Kano:

Babbar magana ai wadanan dai sun hada kansu da wahala da kuma da-na-sani dan kishi dai babu komai a cikinsa sai wahala. To, shashanci ne da rashin sanin ciwon kai. Kishi dai wani halitta ne wani kuwa dorawa kaine, kishiya babu dadi amma ayi hakuri a kau da kai. Sun yi hakuri su kara hakuri.

 

Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, a Jihar Filato:

Babu shakka kishi na zama guba a wajen easy matan, musamman a lokacin da mazajen su za su kara aure. Wasu kan nemi jefa kansu ga fushin ubangiji ta hanyar kokarin tilastawa mazajen su jingine bukatar su, ta kara aure, amma kuma su kawar da kai daga halayyar sa ta neman mata a waje. Sannan su a karan kansu, idan ma ba su sha guba sun hallaka kansu ba, suna shiga malamai, matsafa, da ‘yan tsibbu, wadanda ke aikata shirka, don neman biyan bukatun su. Akwai wadanda sanadiyyar kishi suke gamuwa da ciwon hawan jini da ciwon zuciya, ko matsalar kwakwalwa.

 

Sunana Princess Fatima Mazadu, Goben Nijeriya:

Kishi kam masifa ce babba, soyayya da kauna ke janyo wa wasu kishi, wasu kuma kwadayin dukiya da kyle-kyelen duniya. Danganta kansu ga mutuwa a kowani lokaci namiji bai zamo lallai ya rigata mutuwa ba, sannan mace ta sani lallai kishi halitta ce, amma bai halarta akan auren wata har ya zamo kin iya kashe kanki ba ko saboda abun duniya. Shawarata a nan su rage mummunan kishi, su nemi na kansu, su zamo masu godiya da kulawa a rayuwa wasu matan ko auren ma babu bare kwadayin dukiya da kishi.

 

Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:

Tabbas ana samun mata masu kishin da ya wuce hankali saboda son zuciya kuma gaskiya makomarsu bata kyau. Kishi dabi’ace da Allah ya halicci mata akai har ma wasu mazan ya kamata su nuna kishinsu ta hanya mafi kyau lokacin da mijinsu zai kara aure kuma su sani da ba a auren da suma ba a aurosu ba. Shawara a nan ita ce kowa ya ji tsoron Allah akan hakan.

 

Sunana Hauwa Abubakar Sarki, daga Suleja Jihar Neja:

Kishiya halitta ce sai dai kowa da yadda yake sarrafa nasa kalar kishin, har kullum muna kira ga matan da suke da tsanani kishi da kar su bari kishi ya rufe masu ido har ya kai ga sun aikata abun da za su zo suna da-na-sani. Biyewa Zuciya, kuma sannan a dabi’ar dan namiji baya son macen da ta cika tsanani kishi. Kishi wata aba ce da ubangiji ke halittar bawa da shi ba tare da ya sani ba. Tsananta addu’a da mika al’amura ga ubangiji a yayin da mijinki ya zo maki da zancen kara aure, dole za ki ji babu dadi a ranki amma in ki ka dage da addu’a sai komai ya zo cikin sauki. Shawara ta kada mu bari zukatanmu ya zamana ita ke sarrafa mu ba mu ke sarrafa ta.

Kishi
Rabi'at Sidi Bala
+ posts Bio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A
Kishi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
Taskira

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure
Taskira

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

June 6, 2026
Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
Taskira

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki

May 29, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu

Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.