• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan na karanta wani rahoto mai ban sha’awa da ya yi bayani a kan yadda karancin malaman darussan turanci da lissafi ke kassara samun ilimi mai inganci daga tushe.

Abokin aikina da ya rubuta rahoton, Samuel Abulude ya zakulo matsalolin da suke addabar ilimi da kuma kwazon dalibai a makarantun Firamare da Sakandare a Nijeriya, inda ya dora alhakin lamarin a kan karancin Malaman Turanci da na Lissafi a makarantun fadin tarayyar Nijeriya.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Wani Alhaji Ya Sake Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta A Makkah

Ba abin da za a boye ba ne batun rashin ingancin ilimi a Nijeriya, domin kuwa a shekarun da suka gabata; kasafin kudi na shekara-shekara na gwamnatocin tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi, ya yi matukar raguwa, musamman idan aka duba shawarar kason da majalisar dinkin duniya da hukumominta suka ba da shawarar a rika ware wa sashen na ilimi.

Hukumar ilimi, kimiyya da al’adu ta majalisar dinkin duniya (UNESCO), ta ba da shawarar mambobin hukumar su ware kashi shida na kudaden da suka shigo ko kuma kashi 15 zuwa 20 na kasafin kudin shekara, domin tallafa wa ilimi. Sai dai kamar yadda hukumar ta UNESCO ta bayyana, “Yawancin kasashe har zuwa yanzu ba su aiwatar da wannan shawara da aka ba su ba, wadda za ta taimaka wajen bunkasa ilimi”.

Mafi yawancin manyan makarantun Firamare da Sakandare na fama da wadannan matsaloli, yayin da hukumomin da wadanda abin ya shafa suka yi buris da al’amarin, misali kamar hukumomin Jami’o’i na kasa da kuma na ilimin bai-daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

Har ila yau, hukumar ilimin bai-daya ta shirya taron kara wa juna sani na tsawon kwana biyu, wanda ya hada kwamitin ilimi na majalisar dattawa da jami’an ma’aikatar ilimi ta kasa, a kan wannan karanci na malaman Turanci da Lissafi, wanda kai tsaye ke shafar ingancin ilimi a dukkanin fadin Nijeriya.

A makarantun sakandare, ana ci gaba da fuskantar wannan matsala ta rashin ingancin koyarwa, wanda hakan ke matukar shafar dalibai tare da yi musu tasiri a rayuwarsu.

Babu shakka, wannan matsala ta zama ruwan dare shekara da shekaru, wanda hakan ya kan yi tasiri matuka a kan matasa masu tasowa a halin yanzu. Duk irin abubuwan da suka koya, walau masu kyau ko akasin haka; na iya yin tasiri a rayuwarsu, domin suna kan wata gaba ce ta zama manyan gobe.

A irin wannan yanayin ne, ake koya musu yadda za su rika yin karatu, ya kasance kuma karatun yana shiga kwakwalwarsu da yadda za su ci abinci da kuma yadda za a reni kwazonsu ta hanyar yin la’akari da yadda suke, sannan da kuma yadda za su kyamaci yin ta’ammali da miyagun kwayoyi da dai sauran makamantansu.

Wata mai makaranta mai zaman kanta a Minna, Jihar Neja Olamide Alalade, ta yi magana ne dangane da lamarin inda ta ce, “batun rashin malaman Lissafi da na Turanci a makarantu, na da alaka ne kai tsaye da rashin daukar matakan da suka kamata a dauka. A cewar tata, kamata ya yi mu sake yin tunani kan yadda zamu rika tafiyar da al’amuranmu kamar yadda sauran kasashen waje ke tafiyar da nasu a kan wannan harka ta ilimi”.

Da take yin karin bayani Alalade cewa ta yi, al’umma na yi wa harkar ilimin rikon sakainar kasha, ko kuma sha yanzu magani yanzu, maimaikon daukar matakan da suka dace; wadanda za su taimaka wajen cin moriyar al’amarin kwarai da gaske.

Magana ta gaskiya ita ce, gwamnati da sauran al’umma ya kamata su bada gudunmawar da ta dace, musamman wajen bayar da gudunmayar kudade, domin ilmantar da ‘ya’yansu.Ta ce, “koma me al’umma suka yi; indai bat a da niyyar sa kudade da yawa a wannan bangare na ilimi; a nan gaba, wato shekaru masu zuwa babu wani abin kirki da za a sa ran gani, domin duk wasu abubuwan da aka fara ba za a dauke su da muhimmanci ba, illa ma daga karshe a samu sun lalace’’.

Hadin Sabulu Na Musamman


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

Next Post

Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

Related

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

3 days ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

1 week ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

1 week ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

1 week ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

2 weeks ago
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya
Ilimi

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

2 weeks ago
Next Post
Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.