ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ilimi

A kwanan nan na karanta wani rahoto mai ban sha’awa da ya yi bayani a kan yadda karancin malaman darussan turanci da lissafi ke kassara samun ilimi mai inganci daga tushe.

Abokin aikina da ya rubuta rahoton, Samuel Abulude ya zakulo matsalolin da suke addabar ilimi da kuma kwazon dalibai a makarantun Firamare da Sakandare a Nijeriya, inda ya dora alhakin lamarin a kan karancin Malaman Turanci da na Lissafi a makarantun fadin tarayyar Nijeriya.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Wani Alhaji Ya Sake Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta A Makkah

Ba abin da za a boye ba ne batun rashin ingancin ilimi a Nijeriya, domin kuwa a shekarun da suka gabata; kasafin kudi na shekara-shekara na gwamnatocin tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi, ya yi matukar raguwa, musamman idan aka duba shawarar kason da majalisar dinkin duniya da hukumominta suka ba da shawarar a rika ware wa sashen na ilimi.

ADVERTISEMENT

Hukumar ilimi, kimiyya da al’adu ta majalisar dinkin duniya (UNESCO), ta ba da shawarar mambobin hukumar su ware kashi shida na kudaden da suka shigo ko kuma kashi 15 zuwa 20 na kasafin kudin shekara, domin tallafa wa ilimi. Sai dai kamar yadda hukumar ta UNESCO ta bayyana, “Yawancin kasashe har zuwa yanzu ba su aiwatar da wannan shawara da aka ba su ba, wadda za ta taimaka wajen bunkasa ilimi”.

Mafi yawancin manyan makarantun Firamare da Sakandare na fama da wadannan matsaloli, yayin da hukumomin da wadanda abin ya shafa suka yi buris da al’amarin, misali kamar hukumomin Jami’o’i na kasa da kuma na ilimin bai-daya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Har ila yau, hukumar ilimin bai-daya ta shirya taron kara wa juna sani na tsawon kwana biyu, wanda ya hada kwamitin ilimi na majalisar dattawa da jami’an ma’aikatar ilimi ta kasa, a kan wannan karanci na malaman Turanci da Lissafi, wanda kai tsaye ke shafar ingancin ilimi a dukkanin fadin Nijeriya.

A makarantun sakandare, ana ci gaba da fuskantar wannan matsala ta rashin ingancin koyarwa, wanda hakan ke matukar shafar dalibai tare da yi musu tasiri a rayuwarsu.

Babu shakka, wannan matsala ta zama ruwan dare shekara da shekaru, wanda hakan ya kan yi tasiri matuka a kan matasa masu tasowa a halin yanzu. Duk irin abubuwan da suka koya, walau masu kyau ko akasin haka; na iya yin tasiri a rayuwarsu, domin suna kan wata gaba ce ta zama manyan gobe.

A irin wannan yanayin ne, ake koya musu yadda za su rika yin karatu, ya kasance kuma karatun yana shiga kwakwalwarsu da yadda za su ci abinci da kuma yadda za a reni kwazonsu ta hanyar yin la’akari da yadda suke, sannan da kuma yadda za su kyamaci yin ta’ammali da miyagun kwayoyi da dai sauran makamantansu.

Wata mai makaranta mai zaman kanta a Minna, Jihar Neja Olamide Alalade, ta yi magana ne dangane da lamarin inda ta ce, “batun rashin malaman Lissafi da na Turanci a makarantu, na da alaka ne kai tsaye da rashin daukar matakan da suka kamata a dauka. A cewar tata, kamata ya yi mu sake yin tunani kan yadda zamu rika tafiyar da al’amuranmu kamar yadda sauran kasashen waje ke tafiyar da nasu a kan wannan harka ta ilimi”.

Da take yin karin bayani Alalade cewa ta yi, al’umma na yi wa harkar ilimin rikon sakainar kasha, ko kuma sha yanzu magani yanzu, maimaikon daukar matakan da suka dace; wadanda za su taimaka wajen cin moriyar al’amarin kwarai da gaske.

Magana ta gaskiya ita ce, gwamnati da sauran al’umma ya kamata su bada gudunmawar da ta dace, musamman wajen bayar da gudunmayar kudade, domin ilmantar da ‘ya’yansu.Ta ce, “koma me al’umma suka yi; indai bat a da niyyar sa kudade da yawa a wannan bangare na ilimi; a nan gaba, wato shekaru masu zuwa babu wani abin kirki da za a sa ran gani, domin duk wasu abubuwan da aka fara ba za a dauke su da muhimmanci ba, illa ma daga karshe a samu sun lalace’’.

Hadin Sabulu Na Musamman

Ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.