ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (1)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ilimi

A kwanan nan na karanta wani rahoto mai ban sha’awa da ya yi bayani a kan yadda karancin malaman darussan turanci da lissafi ke kassara samun ilimi mai inganci daga tushe.

Abokin aikina da ya rubuta rahoton, Samuel Abulude ya zakulo matsalolin da suke addabar ilimi da kuma kwazon dalibai a makarantun Firamare da Sakandare a Nijeriya, inda ya dora alhakin lamarin a kan karancin Malaman Turanci da na Lissafi a makarantun fadin tarayyar Nijeriya.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta
  • Wani Alhaji Ya Sake Mayar Da Makudan Kudaden Da Ya Tsinta A Makkah

Ba abin da za a boye ba ne batun rashin ingancin ilimi a Nijeriya, domin kuwa a shekarun da suka gabata; kasafin kudi na shekara-shekara na gwamnatocin tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi, ya yi matukar raguwa, musamman idan aka duba shawarar kason da majalisar dinkin duniya da hukumominta suka ba da shawarar a rika ware wa sashen na ilimi.

ADVERTISEMENT

Hukumar ilimi, kimiyya da al’adu ta majalisar dinkin duniya (UNESCO), ta ba da shawarar mambobin hukumar su ware kashi shida na kudaden da suka shigo ko kuma kashi 15 zuwa 20 na kasafin kudin shekara, domin tallafa wa ilimi. Sai dai kamar yadda hukumar ta UNESCO ta bayyana, “Yawancin kasashe har zuwa yanzu ba su aiwatar da wannan shawara da aka ba su ba, wadda za ta taimaka wajen bunkasa ilimi”.

Mafi yawancin manyan makarantun Firamare da Sakandare na fama da wadannan matsaloli, yayin da hukumomin da wadanda abin ya shafa suka yi buris da al’amarin, misali kamar hukumomin Jami’o’i na kasa da kuma na ilimin bai-daya.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Har ila yau, hukumar ilimin bai-daya ta shirya taron kara wa juna sani na tsawon kwana biyu, wanda ya hada kwamitin ilimi na majalisar dattawa da jami’an ma’aikatar ilimi ta kasa, a kan wannan karanci na malaman Turanci da Lissafi, wanda kai tsaye ke shafar ingancin ilimi a dukkanin fadin Nijeriya.

A makarantun sakandare, ana ci gaba da fuskantar wannan matsala ta rashin ingancin koyarwa, wanda hakan ke matukar shafar dalibai tare da yi musu tasiri a rayuwarsu.

Babu shakka, wannan matsala ta zama ruwan dare shekara da shekaru, wanda hakan ya kan yi tasiri matuka a kan matasa masu tasowa a halin yanzu. Duk irin abubuwan da suka koya, walau masu kyau ko akasin haka; na iya yin tasiri a rayuwarsu, domin suna kan wata gaba ce ta zama manyan gobe.

A irin wannan yanayin ne, ake koya musu yadda za su rika yin karatu, ya kasance kuma karatun yana shiga kwakwalwarsu da yadda za su ci abinci da kuma yadda za a reni kwazonsu ta hanyar yin la’akari da yadda suke, sannan da kuma yadda za su kyamaci yin ta’ammali da miyagun kwayoyi da dai sauran makamantansu.

Wata mai makaranta mai zaman kanta a Minna, Jihar Neja Olamide Alalade, ta yi magana ne dangane da lamarin inda ta ce, “batun rashin malaman Lissafi da na Turanci a makarantu, na da alaka ne kai tsaye da rashin daukar matakan da suka kamata a dauka. A cewar tata, kamata ya yi mu sake yin tunani kan yadda zamu rika tafiyar da al’amuranmu kamar yadda sauran kasashen waje ke tafiyar da nasu a kan wannan harka ta ilimi”.

Da take yin karin bayani Alalade cewa ta yi, al’umma na yi wa harkar ilimin rikon sakainar kasha, ko kuma sha yanzu magani yanzu, maimaikon daukar matakan da suka dace; wadanda za su taimaka wajen cin moriyar al’amarin kwarai da gaske.

Magana ta gaskiya ita ce, gwamnati da sauran al’umma ya kamata su bada gudunmawar da ta dace, musamman wajen bayar da gudunmayar kudade, domin ilmantar da ‘ya’yansu.Ta ce, “koma me al’umma suka yi; indai bat a da niyyar sa kudade da yawa a wannan bangare na ilimi; a nan gaba, wato shekaru masu zuwa babu wani abin kirki da za a sa ran gani, domin duk wasu abubuwan da aka fara ba za a dauke su da muhimmanci ba, illa ma daga karshe a samu sun lalace’’.

Hadin Sabulu Na Musamman

Ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

Hadin Sabulu Na Gyaran Fata (2)

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.