• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zai Iya Shafar Zaben Gwamnoni

by Sabo Ahmad
3 years ago
Zaben shugaban kasa

Masu iya magana na cewa, daga na gaba ake ganin zurfin ruwa. Sakamakon zaben da aka bayyana wanda dantakar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya samu nasarar lashe wa, zai yi matukar tasiri wajen zaben gwamnoni da ‘yan majalisa wanda za ayi nan gaba kadan.

Sau da yawa, wasu masu zabe a jihohi kan jira, su ga jam’iyyar da ta samu nasara a matakin shugaban kasa, su goya mata baya, domin samun su ga ba a bar su a baya ba.

  • INEC Za Ta Bai Wa Tinubu Takardar Shaidar Lashe Zabe Da Yamma

Sakamakon zaben da aka bayyana na cewa, dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ne ya lashe zabe, da kuri’a ma fi yawa tsakaninsa da abokan takararsa, wato Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na jam’iyyar LP, sannan kuma akwai, dan takara jam’iyyar NNPP, wato Injiya Rabi’u Musa Kwankwaso.

Duk da irin talin matsin lambar da al’umma ke ciki, sun fito sosai wajen jefa kuri’arsu ga dan takarar da suke bukata, wannan ma ta sa kowane dan takara ya kwashi na sa rabon, wanda kuma hakan ta sa aka samu wanda ya fi samun rabo mai yawa, kuma aka bayyana shi a matsayin wanda ya samu nasarar lashe wannan zabe.

Wani abin sha’awa shi ne, yadda ba a samu wani rahoto da ke nuna tashin hanlai ba, bayan bayyana sakamakon zaben da aka yi. Yanzu haka dai kallo ya koma sama yayin da ake jiran nan da kwani kadan masu zuwa a yi zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha.
Saboda haka, ake fatan dukkan zabukan da za su biyo baya, su zama an yi su, ba tare da wata hatsaniya ba, wadda za iya haifar da matsaloli a cikin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Zaben da za a yi na gwamnoni da na ‘yanmajalisa, zabe ne wanda yake kusa da jama’a fiye da zaben shugaban kasa, wanda aka yi. Saboda haka tun ganin yadda sakamakon wannan zaben na shugaban kasa,ya sa wasu gwamnonin cewa, dole su sauya taku.

Sai dai wani abu da aka luara da shi, wanda ya hana tasirin yin madudi a wannan zabe shi, matsalar kudi, wadda ta hana wasu ‘yansiyasa amfani da kudi wajen ganin an zabe su.

Ana ganin irin wannan matsalar ta rashin kudi, za ta yi tasiri sosai wajen ganin, ‘yan siyasa basu yi amfani da kudade ba wajen ganin an zabe su.

Zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi, zabe ne, wanda al’ummar kasar nan yanzu haka suke sauraron zuwansa nan da kwanaki kadan masu zuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Nijeriya

Zaben 2023: Shawarwarin ‘Yan Nijeriya Ga Wadanda Suka Ci Da Wadanda Suka Fadi Zabe

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.