ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zai Iya Shafar Zaben Gwamnoni

by Sabo Ahmad
3 years ago
Zaben shugaban kasa

Masu iya magana na cewa, daga na gaba ake ganin zurfin ruwa. Sakamakon zaben da aka bayyana wanda dantakar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya samu nasarar lashe wa, zai yi matukar tasiri wajen zaben gwamnoni da ‘yan majalisa wanda za ayi nan gaba kadan.

Sau da yawa, wasu masu zabe a jihohi kan jira, su ga jam’iyyar da ta samu nasara a matakin shugaban kasa, su goya mata baya, domin samun su ga ba a bar su a baya ba.

  • INEC Za Ta Bai Wa Tinubu Takardar Shaidar Lashe Zabe Da Yamma

Sakamakon zaben da aka bayyana na cewa, dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ne ya lashe zabe, da kuri’a ma fi yawa tsakaninsa da abokan takararsa, wato Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na jam’iyyar LP, sannan kuma akwai, dan takara jam’iyyar NNPP, wato Injiya Rabi’u Musa Kwankwaso.

ADVERTISEMENT

Duk da irin talin matsin lambar da al’umma ke ciki, sun fito sosai wajen jefa kuri’arsu ga dan takarar da suke bukata, wannan ma ta sa kowane dan takara ya kwashi na sa rabon, wanda kuma hakan ta sa aka samu wanda ya fi samun rabo mai yawa, kuma aka bayyana shi a matsayin wanda ya samu nasarar lashe wannan zabe.

Wani abin sha’awa shi ne, yadda ba a samu wani rahoto da ke nuna tashin hanlai ba, bayan bayyana sakamakon zaben da aka yi. Yanzu haka dai kallo ya koma sama yayin da ake jiran nan da kwani kadan masu zuwa a yi zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha.
Saboda haka, ake fatan dukkan zabukan da za su biyo baya, su zama an yi su, ba tare da wata hatsaniya ba, wadda za iya haifar da matsaloli a cikin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Zaben da za a yi na gwamnoni da na ‘yanmajalisa, zabe ne wanda yake kusa da jama’a fiye da zaben shugaban kasa, wanda aka yi. Saboda haka tun ganin yadda sakamakon wannan zaben na shugaban kasa,ya sa wasu gwamnonin cewa, dole su sauya taku.

Sai dai wani abu da aka luara da shi, wanda ya hana tasirin yin madudi a wannan zabe shi, matsalar kudi, wadda ta hana wasu ‘yansiyasa amfani da kudi wajen ganin an zabe su.

Ana ganin irin wannan matsalar ta rashin kudi, za ta yi tasiri sosai wajen ganin, ‘yan siyasa basu yi amfani da kudade ba wajen ganin an zabe su.

Zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi, zabe ne, wanda al’ummar kasar nan yanzu haka suke sauraron zuwansa nan da kwanaki kadan masu zuwa.

Zaben shugaban kasa
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Nijeriya

Zaben 2023: Shawarwarin ‘Yan Nijeriya Ga Wadanda Suka Ci Da Wadanda Suka Fadi Zabe

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.