• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Saran Macizai Ya Addabi Al’ummar Filato Da Gombe

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Saran Macizai Ya Addabi Al’ummar Filato Da Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon ambaliyar ruwar da ta auku a daminar bana, ana ci gaba da samun rahotannin yadda saran macizai a fadin kasar nan ke addabar jama’a sakamakon yawaitar fitowar dabbobi masu rarrafe daga ramukansu inda lamarin ya fi addabar jihohin Filato da Gombe.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa, saran macizai na kara jefa al’ummomi da dama cikin fargaba da hatsari gami da tashin hankali.

  • Xi Ya Jaddada Bukatar Inganta Farfado Da Yankunan Karkara
  • Barazanar Kai Hari Abuja: Buhari Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Kwantar Da Hankalinsu

Lokuta daban-daban mutane na rasa yadda za su je cibiyar jinya domin neman makarin macizai a lokacin da suka gamu da saransu.

Sannan, maciji na iya tsitta yawu ga mutum wanda yawun nasa mai hatsari ne sosai ga mutane.

A bias yawaitar fitowa daga daji da macizai ke yi sakamakon yawan ruwan da ke addabarsu, jama’a kuma na shiga cikin hatsari sakamakon yaduwa da macizan da kuma yawaitar saransu da suke yi.

Labarai Masu Nasaba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

A ziyarar da wakilan kamfanin dillacin labarai suka kai zuwa cibiyoyin kula da saran macizai da kuma jinyar wadanda suka gamu da saran, sun gano cewa an samu karuwar ke sa ke san saran macizai sosai, yayin da aka samu karuwar mutuwar mutane a bias wannan saran a cibiyoyin jinya daban-daban.

Daga cikin wadanda saran macizai ya kashe har da matar sarkin Magama da ke kudancin karamar hukumar Langtang ta jihar Filato.

“Tabbas zan tabbatar maka cewa an samu karuwar saran macizai, daga cikin wadanda tsautsayin saran macizai ya shafa har da matar sarkin Magama.

“Lamari ne mai ban tsoro da firgici matuka. Macizai da dabbobi masu rarrafe su na guduwa ga ambaliyar ruwa kuma suna samun artabu a hanya sa’ilin da suke neman wurin fakewa,” a cewar Dakta Nandul Durfa.

Durfa, babban manajan gudanarwa na kamfanin Echitap, masu sarrafa da maganin kashe (makari) dafin saran Macizai, ya nuna takaicinsa kan yadda ake samun asarar rayuka sakamakon saran Macizai.

Tsohon Shugaban asibiti (CMD) na jami’ar koyarwa ta Abuja ya nuna damuwa da takaicin yadda ake samun karancin maganin kashe dafin saran Macizai a cibiyoyin jinya.

Sannan da yake magana, Dakta Abubakar Saidu Balla, jami’in Nazari da bincike na asibitin kula da makarin saran Macizai da ke Kaltungo a jihar Gombe, ya yi karin haske sosai kan lamarin tare da neman a dauki matakan shawo kan matsalar.

“Sabili da ambaliyar ruwa, gonakai da filaye sun jike sharkaf, sannan macizai na garzayawa zuwa manyan tudu domin neman mafaka inda suke haduwa da mutane.

“Wannan matsalar ta yi kamari sosai musamman yankunan kogunan da suke Borno, Adamawa, Kogi, Gombe da jihar Bauchi.

“Ambaliyar tana tilasta wa macizai kaura daga inda suke zuwa neman wani waje da har hakan kan kai su zuwa dazuka, gidajen mutane ko wuraren daruwa ke taruwa.

“Karin babbar matsala ma a nan shi ne, da dama daga cikin wadanda saran macizai ke shafa ba su iya zuwa asibitocin da ake kula da irin jinyar sakamakon lalacewar hanyoyin ko marashin kyan hanya da gadojin da za su fito da su daga yankunan da suke ko saran macijin ya same su. Kuma, ana samun hakan ne ko ta sanadiyyar ruwa ya yi awun gaba da gadoji da lalata hanyoyin.

“Kamar a yankunan karkara, an saba ceto irin wadannan mutanen ta amfani da mashina, amma mashinan ba su iya taimaka ma wasu sakamakon cewa tukin ma ba yiyuwa yake yi a cikin ruwa. A takaice, da dama daga cikin wadanda suke gamu da irin wannan lamarin nasarar maciji kafin a kai su cibiyar jinya sun mutu.”

Balla ya kara da cewa, yanzu zuwa gonakai na zama wa manoma da farga ma musamman a yankin Gombe.

LEADERSHIP Hausa ta nakalto cewa, Langtang wata karamar hukuma ce da ake yawan samun saran macizai.

Mazauna yankin a duk shekara sukan cire rai kawai saboda yawaitar saran macizai, kuma har zuwa yanzu suna zaman jiran tallafin gwamnati kan wannan lamarin.

Wata mazauniyar yankin, Naomi Bako, wacce ta misalta cewa kauyuka da dama a karamar hukumar suna fuskantar wannan matsalar ta saran macizai, “Muna da cibiyar kula da majinyatar saran macizai a Zamko. Babu wata shekara da za ta wuce da ba ka samu adadin kesa-kesan saran macizai sama da 1,500 ba. A wannan shekarar malamarin bai canza ba.

“Ko a satin da ta gabata, na ga mutum biyu da aka kai asibitin da suke fama da saran macizai.”

Kazalika, Shugaban kungiyar Mafarauta na karamar hukumar Josta Gabas, Atsen Daniel, ya ce jama’a ayankin na fama da matsalar yawaitar saran macizai, kuma hakan na zama abun fargaba ga al’umma.

Daniel ya ce, “Abun da zan iya cewa shi ne akwai kesa-kesan saran macizai a yankunanmu. Ban san adadin mutanen da lamarin ya shafa ba zuwa yanzu, amma a matsayina na shugaban mafarauta na san akwai rahoton wadanda saran ya shafa da yawa.”

Ya kara da cewa, sau tari a duk shekara a lokacin damina ana samun yawaitar saran macizai, kuma hakan bai rasa nasaba da ruwan da ke yawan yi da ke fitar da macizan daga dazuka zuwa neman mafaka.

Ya ce, “Macizai na yawan neman mafaka a damina, kuma da wuya garesu su samu wurin da bai jike ba su zauna domin gudanar da rayuwansu, sannan, a lokacin rani kuma sun fi son zama wurin da ke da sanyi. Mu ba tsoron macizai muke ba. Mun san cewa macizai na zama abu mai hatsari idan ya sari mutum.”

Sannan, wani Farfesa a fannin yanayi kasa, Farfesa Olaniran Olajire, da tsohon shugaban NIB, Sunday Wusu, sun nuna bukatar da ke akwai da cewa gwamnatoci a dukkanin matakai da su karfafi yawaitar dashen itatuwa domin dakile ambaliyar ruwa a nan gaba.

Suka ce, matsalar ambaliyar ruwa a sassan kasar nan na faruwa ne sakamakon canjin yanayi don haka suka nuna bukatar karfafa matan da suka dace na kariya daga wannan matsalar.

Ambaliyar ruwa wadda akalla ya jefa ‘yan Nijeriya miliyan 2.5 ciki har da yara miliyan 1.5 cikin hatsari a cewar rahoton asusun kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya (UNICEF),wanda ya janyo mutuwar mutum sama da 600 da tilasta wa sama da miliyan 1.4 kaura daga muhallansu.

Da ya ke magana kan wannan lamarin, Olajire, ya shaida cewar dumamar yanayi na bukatar daukan matakan gaggawa, don haka ne ya nemi gwamnati da ta tashi tsaye wajen yin abubuwan da suka dace kan lamarin.

Wani rahoton da hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO) ta taba fitarwa ya nuni da cewa, kimanin mutum miliyan 5.4 ne dai maciji kan sara a duk shekaraa duniya, adadin wadanda kan rasa rayukansu kuma ya kama daga 81,000zuwa 130,000.

Akwai kuma mutane da dama da ke rasa gabbansu da kuma nakasa sanadiyyar saran macijizai. Nijeriya dai na daya daga cikin kasashen da macizai ke barna sosai.

Al’ummomi da dama a kasar dai na rayuwa ne kullum cikin fargaba saboda da matsalar saran majici, musamman yanzu lokaci damina zuwa kaka.

Manoma da kuma kananan yara ne matsalar ta fi shafa. Da dama daga cikinsu a kan kai su asibitin jinyar sarar maciji ne da ke garin Kaltungo, daya daga cikin cibiyoyi kalilan na musamman domin jinyar sarar maciji da ake da su a kasar nan.

Wata babbar matsalar dai ita ce yadda wadanda macijin kan sara ba sa samun magani yadda ya kamata.

Wasu lokuta dai magani kan kare karkaf a cibiyar ta Kaltungo, amma akullum marasa lafiya sai kwarara suke yi domin neman maganin.

Kuma masana na cewa samar da magani a kan kari da kuma kai duk wanda maciji ya sara asibiti da wuri za su taimaka matuka wajen rage yawan mace-macen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaAsibitiFilatoGombeMacizaiMagani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Ake Fama Da Karancin Mai A Abuja – IPMAN

Related

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

3 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

7 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

11 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

13 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

14 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

18 hours ago
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Ake Fama Da Karancin Mai A Abuja – IPMAN

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Ake Fama Da Karancin Mai A Abuja – IPMAN

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.