• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya

by Bello Hamza
1 year ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
Yadda Talauci Da Jahilci Ke Kara Yawaitar Safarar Sassan Jikin Dan Adam A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yanzu da bukatar dashen koda da hanta suke kara karuwa a musamman a kasashe masu tasowa, ana nuna damuwa a kan yadda safarar sassan jikin dan adam ke karuwa a Nijeriya musamama kuma ga wadanda suka dandana dadin safarar sassan jikin mutanen.

Ana samun karuwar wannan muguwar sana’a a kasashe masu tasowa, musamman a tsakanin mutanen da suke samun kazamin kudi ta hanyar abin a Nijeriya kamar yadda sashin bincike musamman na LEADERSHIP ya gano.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Ya Taya Tebboune Murnar Sake Zama Shugaban Algeria

Masana sun ce harkar cire wani sashi a jiki mutum abu ne da ba shi da kyau kuma yana zama wani nau’i na cin zarafin bil adam, inda ake yaudarar mutane da ke da matsalolin rayuwa a cuce su. Ana bukatar wasu mutane marasa imani wajen aiwatar da wannan muguwar sana’a da ke cire wa mutum sassan jikinsa.

Wasu ‘yan Nijeriyan da lamarin yake damu su sun bukaci dukkan masu ruwa da tsaki a bangaren kiwon lafiya su hada karfi da karfe domin samun nasarar fattatakar safarar sassan jikin da adam a kasar nan.

Biciken LEADERSHIP ya kuma nuna cewa, a kwai alaka a kan yadda ake samun karuwar garkuwa da mutane da karuwar haramtattciyar sana’ar ta safarar sassan jikin mutane a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

Misali a shekarar 2023, wani dalibin Jami’ar Fatakwal ya kashe budurwarsa inda ya cire mata wani sashen jikinta da niyyar yin tsafi da shi. An kuma gano cewa, sashen jikin da aka fi safararsa a Nijeriya shi ne koda.

Bayanai daga cibiyar tattara bayanai da karbar gudunmawa da dashen koda ta ‘Global Database on Donation and Transplantation’ sun nuna cewa a tsakanin shekarar 2015 da 2020, an yi dashen koda fiye da 651 ba bisa ka’ida ba a Nijeriya.

An kiyasta cewa, safarar sassan mutum ba bisa ka’ida ba a duniya na samar da tsakanin Dala miliya 840 da dala biliyan 1.7 a duk shekara a fadin duniya. Ana kuma sayen koda a kan ‘yan daloli a kasashe masu tasowa, daga bisani a sayar tsakanin dala 20,000 zuwa 30,000 a kasashen da suka ci gaba. An kuma kiyasta yin dashen koda fiye da 129,681 a shekarar 2020 kawai, inda aka samu koda 36,125 daga wadada suka mutu. Wannan ke nuna ana yin dashen koda akalla 15 a kusan duk awa 1 a duniya.

Saboda tsanannin rayuwa, a yanzu wasu ‘yan Nijeriya da dama suna sayar da wasu sassan jikinsu masu muhimmaci wanda hakan yana sanya rayuwarsu a cikin hadari. Wasu matan Nijeriya na shan wasu kwayoyi domin ya haifar musu da wani yanayi da kwan jikinsu zai bunkasa daga nan sai su sayar da su ga cibiyoyin bincike. Wasu dalibai mata na jami’a suna kuma sayar da kwan haihuwarsu ga masu bukata, masu amfani da shi wajen samar da jarirai ta fasahar ‘IBF’.

Ba kamar yadda abin yake a manyan kasashe ba, mata ke bayar da kwansu a karkashin kulawa da sa idon dokoki, amma a Nijeriya kananan ‘yan mata na sayar da kwansu kusan akalla a kan Naira 50,000.

An kuma samu wasu rahottanin da ke nuna yadda ake tilasta wa ‘yan mata sayar da kwansu a kan dan kudin da bai kai ya kawo ba. Akwai rahottanin kafafen yada labaru da ke nuna cewa, wasu matan masu shekara 16 na sayar da kwansu ba tare da samun jagoranci daga wani wakili ba.

A kwanaki ne, wani magidanci mai suna Olaniyi Iyiol, dan shekara 41 mazaunin Jihar Ondo ya bayyana cewa, talauci ya sa shi yanke shawarar sayar da daya daga cikin kodarsa duk da kuma yana sane da kasadar da ke tattare da dokokin yin haka da kuma yadda abin zai iya shafar lafiyarsa, amma saboda ba shi da wata hanya ta ciyar da iyalansa ya sa ya yanke wannan shawarar.

Wani abin takaii game da wannan lamarin kuma shi ne yadda wasu ‘yan Nijeriya masara imani ke daukar wasu matasa maza da mata daga kauyuka da alkawarin za a samar musu da aikin yi a birane amma cikakken dalin dauko su shi ne a cire musu wasu sassa a jikinsu domin a sayar.

A shekarar da ta gabata, tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu da matarsa Beatrice da wani likita mai suna Dr Obinna Obeta, sun shiga hannu, aka kuma daure su a kasar Birtaniya saboda yaudarar wani matashi mai suna Dabid Nwamini, suka kai shi Birtaniya da niyyar cire masa koda domin a ba ‘yar Ekweremadu Sonia Ekweremadu, wadda ke fama da ciwon koda.

An daure Ekweremadu da abokan burninsa ne na tsawon shekaru a gidan yari bisa laifin safarar mutum zuwa kasar Birtaniya.

Wasu masu ruwa da tsaki sun nuna damuwa a kan yadda ake shigar da likitoci a wanan dambarwar.

A Abuja babbar birnin tarayyar kasar nan, an gano masu safarar sassan jikin mutane ba bisa ka’ida ba, bayan da aka gano wasu gungun masu aikata laifi da suka yaudari wani matashi dan shekara 16 mai suna Yahaya Musa, zuwa asibiti a Abuja tare da cire masa koda.

A wani rahoton da aka yada ta tashar talabijin ta intanet ta LEADERSHIP TB a makon da ya wuce, wani mutum mai suna Malam Musa ya bayyana cewa, an yi masa alkawarin naira miliyan 1 in ya yarda ya bayar da kodarasa. Ya yi bayani ne a mastayin mai bayar da shaida a babbar kotun babbar birnin tarayya Abuja da ke Zuba yayin da ake shari’ar ma’akata 4 na asibitin ‘Alliance Hospital and Serbices Ltd’, wadanda ake zargi da cire sassan jikin mutane ba da cikakken izini ba.

Hukumar yaki da safarar mutane ta (NAPTIP) ta gurfanar da Dr. Christopher Otabor, Emmanuel Olorunlaye, Chikaodili Ugochukwu, and Dr. Aremu Abayomi inda take tuhumar su da laifuka 11 da suka hada da cire sassan jikin dan adam ba tare da izinini ba. Babban lauya, Hassan Dahiru, ya bayyana yadda wadannan jami’an asibitin ke kan gaba wajen cire wa mutane sassan jiki.

Wannan wani misali ne na yadda rashin sanin doka da kuma hadarin da ke tattare da harkar cire sassan jiki ke azalzala lamarin safarar sassan jiki, haka kuma halin talauci da natsin rayuwa yana jefa wasu matasan fadawa tarkon masu safarar sassan jiki.

A martaninsa kan yadda lamarin yake kara kamari, shugaban kungiyar likitocin yankin Abuja, Dr Charles Ugwuanyi, ya nemi a samar da dokar da za ta taka wa masu safarar sassan dan adam birki, ya ce lamarin akwai tashin hankali ta yadda ake amfani da halin matsin rayuwua da talauci da al’umma ke ciki wajen jefa su halin da zai iya kai ga rasa rayukansu

Haka kuma wani abbban likita mai suna Oluwole Adeleke, ya ce a halin yanzu ya kamata masu ruwa da tsaki su shigo domin kawo karshen wannan lamarin gaba daya ba tare da bata lokaci ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaSafaraSassan JikiTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Kusa Ƙaddamar Da Shirin Yarjejeniyar ÆŠa’a Ta Ƙasa, inji Minista 

Next Post

Siffofin Manzon Allah (SAW)

Related

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

4 minutes ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

12 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

17 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da É—umi-É—uminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

20 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

22 hours ago
Next Post
Siffofin Manzon Allah (SAW)

Siffofin Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.