• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 weeks ago
TRCN

Hukumar Rajistar Malamai ta Nijeriya (TRCN) ta nuna damuwa kan yawaitar malaman da ba su cancanta ba a kasar, inda ta bayyana hakan a matsayin babban dalilin raguwar ingancin ilimi.

 

Babban Daraktan TRCN, Dr. Ronke Soyombo ce ta bayyana hakan a ranar Litinin yayin bayyanarta a shirin ‘The Morning Brief na tashar Channels Telebision, a lokacin bikin Ranar Malamai ta Duniya ta 2025, mai taken “Sake Tsara Koyarwa a Matsayin Sana’a ta Hadin Kai.”

 

Dr. Soyombo ta yi bakin ciki da cewa mutane da yawa da ke koyarwa a makarantu a fadin Nijeriya ba su da cancantar da ake bukata don gudanar da aikinsu yadda ya kamata, abin da ya fi shafar makarantu masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

 

“Akwai da yawa malamai marasa cancanta a cikin aikin. Muna da wadanda ke koyarwa a ajujuwa amma ba su da takardun shaidar koyarwa, musamman a makarantu masu zaman kansu,” in ji ta.

 

Ta bayyana cewa, yayin da wasu mutane ke da sha’awar koyarwa da gaske, rashin horo na hukuma ya hana su shiga aikin koyarwa.

 

Dr. Soyombo ta bayyana cewa TRCN a halin yanzu na da malamai masu rijista kusan miliyan 1.4, tare da shirin kara wannan adadi zuwa miliyan 20 cikin shekaru biyu masu zuwa ta hanyar dijital da saurin rajista.

 

“Mun zamanantar da tsarinmu domin mutane da yawa su sami damar yin rijista,” in ji ta. “Kowane malami yana da bai wa ta musamman wadda ta bambanta da ta wani. Amma abin da muke kokarin yi domin inganta ilimi shi ne kowa ya zo tare da tsarinsa na darussa.”

 

“Za ku iya zama malamai uku da ke koyarwa ga rukuni guda na dalibai, kuma idan kuka zo tsara darusa tare tabbas za ku samar da wani abu mai dimbin fa’ida fiye da lokacin da kake aiki kai kadai.”

 

“Babu shakka akwai karancin malamai, don haka abin da muke yi tare da wannan gwamnati shi ne gaggauta shirin Diploma na Kwarewa a Fannin Ilimi (PDE). Ga wadanda ba su da shi, yanzu lokaci ne da za su iya samun dama. Muna gaggauta kwas din zuwa watanni shida ga malamai masu kwarewa, domin da zaran sun kammala, za su sami kwarewa. Wannan zai sa mu samu isassun ma’aikata a fannin koyarwa.”

 

“Abin da TRCN ke yi kuma shi ne duba yadda za mu inganta malamai. Haka kuma, muna tallafa musu da kayan aiki a cikin ajujuwa, domin wasu malamai suna da kwarewa sosai kuma suna neman yadda za su tsara darussa don tallafawa sauran malamai, kuma hakan zai karfafa wasu su shigo,” in ji ta.

 

A halin da ake ciki, Uwargidan Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, a cikin sakonta na Ranar Malamai ta Duniya, ta yaba wa malamai kan gudummawar da ba za a iya misaltawa ba wajen gina kasa, sannan ta yi kira ga kokari na musamman don magance karancin malamai a duniya.

 

Tinubu ta bayyana malamai a matsayin “jarumai, masu tsara tunani, da jagorantar karni,” inda ya jaddada cewa inganta walwalarsu da ci gaban kwarewarsu na aiki shi ne mabudin karfafa tsarin ilimi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.