• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki

by Abubakar Abba
7 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar masu sarrafa magunguna na kasa Oluwatosin Jolayemi ya bayyana cewa, yajin aikin da jami’an hukumar kula da inaganci abinci da magunguna ta Kasa ke ci gaba da yi, ya kara janyo masana’atun gaza kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

Jolayemi ya zayyano manyan ilolin da yajin aikin ya janyo masu sarrafa magungunan, musamman na masana’atun gazawar su ta kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A cewarsa, iadan har masu sarrafa magungunan, ba su samu amincewar hukumar kula da inganci abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ba, to fa, ba za su iya kwashe kayansu daga tashoshin Jiragen ruwan kasar ba.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, yajin aikin jami’an hukumar ya kara tabarbarar da fannin kiwon lafiyar kasar nan, wanda a yanzu, hakan ya jefa fargaba a zukantan ‘yan kasar, a kan inganci magungunan da ake shigowa da su, cikin kasar.

Jami’an hukumar sun tsunduma cikin yajin aikin na sai baba ta gani ne, a karkashin kungiyar manyan ma’aikata da kamfanoni mallakar gwamnati (SSASCGOC) a ranar 7 na watan Okutobar 2024.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Sun tsunduma yajin aikin ne bisa neman a biya masu bukatunsu da suka hada da maido da sakamakon zana jarrabar karin girma ta 2024 a kan maki kashi 35.

Daya bukatar jami’an ita ce, cike guraben Daraktocin hukumar, ianganta tsarin jarrabawa da karin girma ga jami’in sanin halaiyyar ‘yan Adama da kuma biyan su karin albashin da ya kamata ace an biya su da aka dauke su aiki a na 2022.

Sai dai, Jolayemi ya jaddada cewa, kalubalen da masu sarrafa magungunan ke fuskanta, ta zarce yajin aikin da ma’aikatan hukumar NAFDAC, ke ci gaba da yi a yanzu.

A cewarsa, a zahiri maganar ba wai kawai dangane da hukumar ta NAFDAC ba ce, amma maganar ita ce, a kan rashin iya biyan kudaden fiton kayan su da ke a tashoshin Jiragen ruwa na kasar, saboda kalubalen da suka shafi bankuna

Jolayemi ya ci gaba da cewa, “Ko da kuwa hukumar NAFDAC ta warware matsalolinta da jami’anta, mu a namu bangaren za mu ci gaba da fuskantar manyan matsalolin mu na kasa biyan kudaden na fiton kayan mu.”

A cewarsa,“Tun daga kan manya masana’antu masu sarrafa magunguna da kuma kananansu yajin aikin jami’an hukumar ta NAFDAC, ya shafi gudanar da ayyuaknsu.”

Shi ma a na sa bangaren tsohon shugaban kungiyar masu sa ido a kan yadda ake sarrafa magunguna ta kasa (PSN) Olumide Akintayo, ya nuna damuwarsa a kan yajin aikin jami’an na hukumar NAFDAC.

Olumide ya yi nuni da cewa, yajin akin zai zai janyo tsaiko wajen rabar da magunguna a kasar da kuma shigowar magunguna marasa inganci cikin kasar Kazalika ya ce, yajin aikin zai yanyo jinkiri, wajen daukar samfarin magungunna da za a yi gwajinsu a dakin gwaje-gwaje na hukumar NAFDAC, duba da cewa, har yanzu, magungunna da masu sarrafa magungunan suka shigo da su cikin kasar, na jibge a tashoshin Jiragen rawa na kasar.

Ya yi gargadin cewa, yajin aikin zai kara tabarbarar da tafiyar shugabancin da hukumar idan har, ba a yi masalaha ba.

Ya yi kira ga Darakta Janar ta hukumar NAFDAC ta kasa Farfesa Mojisola Adeyeye, da ta lalubo da mafita da jami’anta kan yajin aikin, duba da yadda yajin aikin, ke neman yiwa fannin kiwon lafiyar kasar nakasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NAFDACYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

Next Post

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

Related

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

5 days ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

4 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

1 month ago
Next Post
Yajin Aiki

Kakakin Ma'aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda

May 28, 2025
Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Taron Kolin ASEAN: Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

May 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

May 28, 2025
Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

Mutum 1 Ya Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Abuja

May 28, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

May 28, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

Unity Cup: Yau Nijeriya Da Ghana Zasu Kece Raini A Birnin Landan

May 28, 2025
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

May 28, 2025
Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

May 28, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.