• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki

by Abubakar Abba
8 months ago
in Tattalin Arziki
0
Yajin Aikin Ma’aikatan NAFDAC Ya Kazanta Halin Da Masana’antun Harhada Magunguna Ke Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar masu sarrafa magunguna na kasa Oluwatosin Jolayemi ya bayyana cewa, yajin aikin da jami’an hukumar kula da inaganci abinci da magunguna ta Kasa ke ci gaba da yi, ya kara janyo masana’atun gaza kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

Jolayemi ya zayyano manyan ilolin da yajin aikin ya janyo masu sarrafa magungunan, musamman na masana’atun gazawar su ta kwashe kayansu da suka shigo da su cikin kasar daga tashoshin Jiragen ruwan kasar.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A cewarsa, iadan har masu sarrafa magungunan, ba su samu amincewar hukumar kula da inganci abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ba, to fa, ba za su iya kwashe kayansu daga tashoshin Jiragen ruwan kasar ba.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, yajin aikin jami’an hukumar ya kara tabarbarar da fannin kiwon lafiyar kasar nan, wanda a yanzu, hakan ya jefa fargaba a zukantan ‘yan kasar, a kan inganci magungunan da ake shigowa da su, cikin kasar.

Jami’an hukumar sun tsunduma cikin yajin aikin na sai baba ta gani ne, a karkashin kungiyar manyan ma’aikata da kamfanoni mallakar gwamnati (SSASCGOC) a ranar 7 na watan Okutobar 2024.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Sun tsunduma yajin aikin ne bisa neman a biya masu bukatunsu da suka hada da maido da sakamakon zana jarrabar karin girma ta 2024 a kan maki kashi 35.

Daya bukatar jami’an ita ce, cike guraben Daraktocin hukumar, ianganta tsarin jarrabawa da karin girma ga jami’in sanin halaiyyar ‘yan Adama da kuma biyan su karin albashin da ya kamata ace an biya su da aka dauke su aiki a na 2022.

Sai dai, Jolayemi ya jaddada cewa, kalubalen da masu sarrafa magungunan ke fuskanta, ta zarce yajin aikin da ma’aikatan hukumar NAFDAC, ke ci gaba da yi a yanzu.

A cewarsa, a zahiri maganar ba wai kawai dangane da hukumar ta NAFDAC ba ce, amma maganar ita ce, a kan rashin iya biyan kudaden fiton kayan su da ke a tashoshin Jiragen ruwa na kasar, saboda kalubalen da suka shafi bankuna

Jolayemi ya ci gaba da cewa, “Ko da kuwa hukumar NAFDAC ta warware matsalolinta da jami’anta, mu a namu bangaren za mu ci gaba da fuskantar manyan matsalolin mu na kasa biyan kudaden na fiton kayan mu.”

A cewarsa,“Tun daga kan manya masana’antu masu sarrafa magunguna da kuma kananansu yajin aikin jami’an hukumar ta NAFDAC, ya shafi gudanar da ayyuaknsu.”

Shi ma a na sa bangaren tsohon shugaban kungiyar masu sa ido a kan yadda ake sarrafa magunguna ta kasa (PSN) Olumide Akintayo, ya nuna damuwarsa a kan yajin aikin jami’an na hukumar NAFDAC.

Olumide ya yi nuni da cewa, yajin akin zai zai janyo tsaiko wajen rabar da magunguna a kasar da kuma shigowar magunguna marasa inganci cikin kasar Kazalika ya ce, yajin aikin zai yanyo jinkiri, wajen daukar samfarin magungunna da za a yi gwajinsu a dakin gwaje-gwaje na hukumar NAFDAC, duba da cewa, har yanzu, magungunna da masu sarrafa magungunan suka shigo da su cikin kasar, na jibge a tashoshin Jiragen rawa na kasar.

Ya yi gargadin cewa, yajin aikin zai kara tabarbarar da tafiyar shugabancin da hukumar idan har, ba a yi masalaha ba.

Ya yi kira ga Darakta Janar ta hukumar NAFDAC ta kasa Farfesa Mojisola Adeyeye, da ta lalubo da mafita da jami’anta kan yajin aikin, duba da yadda yajin aikin, ke neman yiwa fannin kiwon lafiyar kasar nakasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NAFDACYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

Next Post

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

2 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

4 weeks ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 months ago
Next Post
Yajin Aiki

Kakakin Ma'aikatar Tsaron Sin Ya Yi Tir Da Sayar Da Makamai Da Amurka Ke Yi Wa Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.