ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Cin Hanci Ta Zama Wata Alama Dake Wakiltar Kasar Sin A Idon ’Yan Nijeriya

by CGTN Hausa
2 years ago
Cin hanci

Yayin zama karo na 3 na kwamitin tabbatar da da’a da ladaftarwa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis na kasar Sin na 20, wanda ya gudana a jiya Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da a jaddada kokarin samun nasara a yaki da cin hanci da rashawa, inda ya ce yaki ne dake bukatar juriya da dauriya.

Yaki da cin hanci da rashawa ya zama tamkar wata alama dake wakiltar kasar Sin da na dade da saninta tun kafin shigowata kasar. Akasari, al’ummar Nijeriya kan yi kwatance da kasar Sin a duk lokacin da aka samu wata badakalar cin hanci dake bukatar ladaftarwa, don haka na taso, na kuma kwan da sanin cewa, kasar Sin kasa ce da ba ta lamuntar wannan mummunar al’ada.

  • Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa A Harkokin Duniya
  • INEC Ta Shirya Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihar Kano

Abun burgewa shi ne, duk da suna da fice da ta yi a bangaren yaki da cin hanci da rashawa, har yanzu kasar Sin ba ta yin kasa a gwiwa wajen tabbatar da ba a mayar da hannun agogo baya ba, kamar yadda muka ji, muka kuma gani a jawabin shugaba Xi Jinping na jiya.

ADVERTISEMENT

A ko da yaushe, kasashenmu masu tasowa kan yi buri da ikirarin neman ci gaba mai inganci da karfafa tattalin arzikinsu, sai dai, babban abun dake ci musu tuwo a kwarya shi ne, cin hanci da rashawa. Wannan matsala ce da ta yi katutu a kasashenmu, domin kowa ya samu dama, to neman gina kansa yake maimakon kasa. Wannan dalili kadai, ya sa muka bambanta da kasar Sin da kuma hanyar da ta dauka na raya kanta.

Muddin kasashenmu na son taka matakin da kasar Sin ta kai a duniya, to dole ne su zage damtse su kuma dauki batun yaki da cin hanci da rashawa da muhimmanci, ta yadda babu wanda zai tsira daga fushin hukuma idan aka same shi da laifi. Haka kuma, a yi kokarin datse matsalar tun daga tushe da kuma kokarin ganin an cusa kyakkyawan akida da kishin kasa a zukatan al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana, yaki da cin hanci, aiki ne dake bukatar hakuri da juriya, haka kuma ba shi da wa’adi, sannan yana bukatar kyakkyawan kuduri na shugabanci. Wadannan dabaru ne da ya kamata kasashenmu dake burin koyi da kasar Sin ya kamata su nazarta, su kuma dauka, domin ta hakan ne kadai, za a kai ga matakin da ake buri da samun al’umma mai kyakkyawar dabi’a da kishin kasa kamar kasar Sin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
Daga Birnin Sin

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
Next Post
Cin hanci

Bayan Ganawa Da Mohammed Bello Koko, Ma’aikatan NPA Sun Janye Shiga Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.