ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Cin Hanci Ta Zama Wata Alama Dake Wakiltar Kasar Sin A Idon ’Yan Nijeriya

by CGTN Hausa
2 years ago
Cin hanci

Yayin zama karo na 3 na kwamitin tabbatar da da’a da ladaftarwa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis na kasar Sin na 20, wanda ya gudana a jiya Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da a jaddada kokarin samun nasara a yaki da cin hanci da rashawa, inda ya ce yaki ne dake bukatar juriya da dauriya.

Yaki da cin hanci da rashawa ya zama tamkar wata alama dake wakiltar kasar Sin da na dade da saninta tun kafin shigowata kasar. Akasari, al’ummar Nijeriya kan yi kwatance da kasar Sin a duk lokacin da aka samu wata badakalar cin hanci dake bukatar ladaftarwa, don haka na taso, na kuma kwan da sanin cewa, kasar Sin kasa ce da ba ta lamuntar wannan mummunar al’ada.

  • Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa A Harkokin Duniya
  • INEC Ta Shirya Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihar Kano

Abun burgewa shi ne, duk da suna da fice da ta yi a bangaren yaki da cin hanci da rashawa, har yanzu kasar Sin ba ta yin kasa a gwiwa wajen tabbatar da ba a mayar da hannun agogo baya ba, kamar yadda muka ji, muka kuma gani a jawabin shugaba Xi Jinping na jiya.

ADVERTISEMENT

A ko da yaushe, kasashenmu masu tasowa kan yi buri da ikirarin neman ci gaba mai inganci da karfafa tattalin arzikinsu, sai dai, babban abun dake ci musu tuwo a kwarya shi ne, cin hanci da rashawa. Wannan matsala ce da ta yi katutu a kasashenmu, domin kowa ya samu dama, to neman gina kansa yake maimakon kasa. Wannan dalili kadai, ya sa muka bambanta da kasar Sin da kuma hanyar da ta dauka na raya kanta.

Muddin kasashenmu na son taka matakin da kasar Sin ta kai a duniya, to dole ne su zage damtse su kuma dauki batun yaki da cin hanci da rashawa da muhimmanci, ta yadda babu wanda zai tsira daga fushin hukuma idan aka same shi da laifi. Haka kuma, a yi kokarin datse matsalar tun daga tushe da kuma kokarin ganin an cusa kyakkyawan akida da kishin kasa a zukatan al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana, yaki da cin hanci, aiki ne dake bukatar hakuri da juriya, haka kuma ba shi da wa’adi, sannan yana bukatar kyakkyawan kuduri na shugabanci. Wadannan dabaru ne da ya kamata kasashenmu dake burin koyi da kasar Sin ya kamata su nazarta, su kuma dauka, domin ta hakan ne kadai, za a kai ga matakin da ake buri da samun al’umma mai kyakkyawar dabi’a da kishin kasa kamar kasar Sin.

Cin hanci
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Cin hanci

Bayan Ganawa Da Mohammed Bello Koko, Ma’aikatan NPA Sun Janye Shiga Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.