ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Cin Hanci Ta Zama Wata Alama Dake Wakiltar Kasar Sin A Idon ’Yan Nijeriya

by CGTN Hausa
3 years ago
Cin hanci

Yayin zama karo na 3 na kwamitin tabbatar da da’a da ladaftarwa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis na kasar Sin na 20, wanda ya gudana a jiya Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da a jaddada kokarin samun nasara a yaki da cin hanci da rashawa, inda ya ce yaki ne dake bukatar juriya da dauriya.

Yaki da cin hanci da rashawa ya zama tamkar wata alama dake wakiltar kasar Sin da na dade da saninta tun kafin shigowata kasar. Akasari, al’ummar Nijeriya kan yi kwatance da kasar Sin a duk lokacin da aka samu wata badakalar cin hanci dake bukatar ladaftarwa, don haka na taso, na kuma kwan da sanin cewa, kasar Sin kasa ce da ba ta lamuntar wannan mummunar al’ada.

  • Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa A Harkokin Duniya
  • INEC Ta Shirya Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihar Kano

Abun burgewa shi ne, duk da suna da fice da ta yi a bangaren yaki da cin hanci da rashawa, har yanzu kasar Sin ba ta yin kasa a gwiwa wajen tabbatar da ba a mayar da hannun agogo baya ba, kamar yadda muka ji, muka kuma gani a jawabin shugaba Xi Jinping na jiya.

ADVERTISEMENT

A ko da yaushe, kasashenmu masu tasowa kan yi buri da ikirarin neman ci gaba mai inganci da karfafa tattalin arzikinsu, sai dai, babban abun dake ci musu tuwo a kwarya shi ne, cin hanci da rashawa. Wannan matsala ce da ta yi katutu a kasashenmu, domin kowa ya samu dama, to neman gina kansa yake maimakon kasa. Wannan dalili kadai, ya sa muka bambanta da kasar Sin da kuma hanyar da ta dauka na raya kanta.

Muddin kasashenmu na son taka matakin da kasar Sin ta kai a duniya, to dole ne su zage damtse su kuma dauki batun yaki da cin hanci da rashawa da muhimmanci, ta yadda babu wanda zai tsira daga fushin hukuma idan aka same shi da laifi. Haka kuma, a yi kokarin datse matsalar tun daga tushe da kuma kokarin ganin an cusa kyakkyawan akida da kishin kasa a zukatan al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana, yaki da cin hanci, aiki ne dake bukatar hakuri da juriya, haka kuma ba shi da wa’adi, sannan yana bukatar kyakkyawan kuduri na shugabanci. Wadannan dabaru ne da ya kamata kasashenmu dake burin koyi da kasar Sin ya kamata su nazarta, su kuma dauka, domin ta hakan ne kadai, za a kai ga matakin da ake buri da samun al’umma mai kyakkyawar dabi’a da kishin kasa kamar kasar Sin.

Cin hanci
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Ka’idojin Na’urar Kiwon Lafiya Ta Sadarwa Tsakanin Kwakwalwa Da Na’ura Mai Amfani Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rokar Gravity-1 Na Kasar Sin Ya Harba Sabbin Taurarin Dan’adam Daga Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Taya Jami’ar Jilin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

September 16, 2026
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing
Daga Birnin Sin

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

September 16, 2026
Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

September 16, 2026
Next Post
Cin hanci

Bayan Ganawa Da Mohammed Bello Koko, Ma’aikatan NPA Sun Janye Shiga Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

September 16, 2026
Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

September 16, 2026
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

September 16, 2026
Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Sojoji Sun Hallaka Wani Jagoran ’Yan Ta’adda A Katsina

September 16, 2026
Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

September 16, 2026
Gwamnatinmu Za Ta Kawar Da Talauci Da Zarar An Zabe Mu – Shettima

Gwamnonin Arewa 6 Kacal Ne Suka Goyi Bayan Tinubu A 2023 – Shettima

September 16, 2026
Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

September 16, 2026
peter

Peter Obi Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Sayi Hannun Jarin Matatar Mai Ta Dangote

September 16, 2026
Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa

Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa

September 16, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 240 Bisa Zargin Laifuka Daban-Daban A Yobe

September 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.