• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Fatara: Gudummawar Sin Da Tasirinta Tsakanin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Fatara

Kudurin kawar da talauci na cikin muhimman bukatun bil adama da tun kaka da kakanni ake hankoron cimma nasararsa. Kuma a duniyar yau, akwai mutane da yawansu ya haura biliyan guda dake rayuwa cikin kangin talauci. Yayin da duniya ke kara dukufa wajen shawo kan wannan matsala, kasar Sin ta yi namijin kokari, wajen samar da damammaki na karfafa gwiwar al’ummun duniya don cimma kyakkyawar rayuwa.

 

A cikin gida, kasar Sin ta yi nasarar tsame sama da al’ummunta miliyan 800 daga kangin talauci, ta kuma yi nasarar cimma kudurin samar da ci gaba mai dorewa, wanda ke cikin ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan da shekarar 2030, tun ma kafin cikar wa’adin ajandar.

  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Mummunar Asara, Ƴan Majalisa 5 Sun Fice
  • Majalisar Wakilai Ta Dakatar Da CBN Daga Sallamar Ma’aikata 1000

Hakan nen ma ya sanya masharhanta da dama ke jinjinawa kwazon kasar a fannin yaki da fatara, musamman ta hanyar dunkule dabarun bunkasa ci gaban tattalin arziki, da manufofin inganta walwalar al’umma. Ta hanyar tsara manufofi daidai da yanayin da ake ciki a sassan kasar daban daban, kasar Sin ta tabbatar da ganin matakan yaki da fatara sun magance takamaiman matsalolin al’ummu mabambanta.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Wannan wani tsari ne da ya taimaka matuka, wajen sauya yanayin wasu sassan kasar da a baya suka yi fama da matsanancin kangin talauci, har ma hakan ya zama misali, kuma abun koyi ga kasashen duniya da dama a wannan fanni.

 

Ga misali, a kasar Rwanda, fasahar noman ciyawar Juncao da kasar Sin ta gabatar, ta taimakawa manoman yankunan karkara, da fasahar noman nau’o’in tsirrai kamar lemar kwado da ciyayin kiwata dabbobi. Hakan ya baiwa manoman kasar damar samun karin kudaden shiga, da samar da yalwar abinci, da tabbatar da ingancin muhalli. Yanzu haka wannan fasaha ta noman Juncao ta shiga kasashen nahiyar Afirka sama da 40, inda a ko ina ake cin gajiyarta.

 

Baya ga batun yaki da fatara, kasar Sin ta gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya” ko BRI, wadda da hadin kan sauran kasashe musamman masu tasowa ake samar da ababen more rayuwa, da raya ilimi da kiwon lafiya. Ko shakka babu wadannan ayyuka sun samar da guraben ayyukan yi, da hade sassa mabambanta wuri guda, da yaukaka ci gaban kowa da kowa, tare da taimakawa wajen tsamo dubban jama’a daga kangin fatara.

 

BRI ta riga ta hallara kasashe da yankunan duniya sama da 160, kana ana aiwatar da manufofinta masu inganci tare da sama da kasashen duniya 150, kuma karkashinta an shigar da kudaden da yawansu ya doshi dalar Amurka biliyan 20, don gudanar da ayyukan raya kasashe sama da 1,100. Wanda hakan ya zamo wata kyakkyawar dama ta ingiza ci gaban kasashe masu tasowa, da sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.