• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Fatara: Gudummawar Sin Da Tasirinta Tsakanin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaki Da Fatara: Gudummawar Sin Da Tasirinta Tsakanin Kasashen Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kudurin kawar da talauci na cikin muhimman bukatun bil adama da tun kaka da kakanni ake hankoron cimma nasararsa. Kuma a duniyar yau, akwai mutane da yawansu ya haura biliyan guda dake rayuwa cikin kangin talauci. Yayin da duniya ke kara dukufa wajen shawo kan wannan matsala, kasar Sin ta yi namijin kokari, wajen samar da damammaki na karfafa gwiwar al’ummun duniya don cimma kyakkyawar rayuwa.

 

A cikin gida, kasar Sin ta yi nasarar tsame sama da al’ummunta miliyan 800 daga kangin talauci, ta kuma yi nasarar cimma kudurin samar da ci gaba mai dorewa, wanda ke cikin ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan da shekarar 2030, tun ma kafin cikar wa’adin ajandar.

  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Mummunar Asara, Ƴan Majalisa 5 Sun Fice
  • Majalisar Wakilai Ta Dakatar Da CBN Daga Sallamar Ma’aikata 1000

Hakan nen ma ya sanya masharhanta da dama ke jinjinawa kwazon kasar a fannin yaki da fatara, musamman ta hanyar dunkule dabarun bunkasa ci gaban tattalin arziki, da manufofin inganta walwalar al’umma. Ta hanyar tsara manufofi daidai da yanayin da ake ciki a sassan kasar daban daban, kasar Sin ta tabbatar da ganin matakan yaki da fatara sun magance takamaiman matsalolin al’ummu mabambanta.

 

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Wannan wani tsari ne da ya taimaka matuka, wajen sauya yanayin wasu sassan kasar da a baya suka yi fama da matsanancin kangin talauci, har ma hakan ya zama misali, kuma abun koyi ga kasashen duniya da dama a wannan fanni.

 

Ga misali, a kasar Rwanda, fasahar noman ciyawar Juncao da kasar Sin ta gabatar, ta taimakawa manoman yankunan karkara, da fasahar noman nau’o’in tsirrai kamar lemar kwado da ciyayin kiwata dabbobi. Hakan ya baiwa manoman kasar damar samun karin kudaden shiga, da samar da yalwar abinci, da tabbatar da ingancin muhalli. Yanzu haka wannan fasaha ta noman Juncao ta shiga kasashen nahiyar Afirka sama da 40, inda a ko ina ake cin gajiyarta.

 

Baya ga batun yaki da fatara, kasar Sin ta gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya” ko BRI, wadda da hadin kan sauran kasashe musamman masu tasowa ake samar da ababen more rayuwa, da raya ilimi da kiwon lafiya. Ko shakka babu wadannan ayyuka sun samar da guraben ayyukan yi, da hade sassa mabambanta wuri guda, da yaukaka ci gaban kowa da kowa, tare da taimakawa wajen tsamo dubban jama’a daga kangin fatara.

 

BRI ta riga ta hallara kasashe da yankunan duniya sama da 160, kana ana aiwatar da manufofinta masu inganci tare da sama da kasashen duniya 150, kuma karkashinta an shigar da kudaden da yawansu ya doshi dalar Amurka biliyan 20, don gudanar da ayyukan raya kasashe sama da 1,100. Wanda hakan ya zamo wata kyakkyawar dama ta ingiza ci gaban kasashe masu tasowa, da sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jam’iyyar Labour Ta Yi Mummunar Asara, Ƴan Majalisa 5 Sun Fice

Next Post

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

6 hours ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

7 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

8 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

9 hours ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

10 hours ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

1 day ago
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.