• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Fatara: Gudummawar Sin Da Tasirinta Tsakanin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaki Da Fatara: Gudummawar Sin Da Tasirinta Tsakanin Kasashen Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kudurin kawar da talauci na cikin muhimman bukatun bil adama da tun kaka da kakanni ake hankoron cimma nasararsa. Kuma a duniyar yau, akwai mutane da yawansu ya haura biliyan guda dake rayuwa cikin kangin talauci. Yayin da duniya ke kara dukufa wajen shawo kan wannan matsala, kasar Sin ta yi namijin kokari, wajen samar da damammaki na karfafa gwiwar al’ummun duniya don cimma kyakkyawar rayuwa.

 

A cikin gida, kasar Sin ta yi nasarar tsame sama da al’ummunta miliyan 800 daga kangin talauci, ta kuma yi nasarar cimma kudurin samar da ci gaba mai dorewa, wanda ke cikin ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan da shekarar 2030, tun ma kafin cikar wa’adin ajandar.

  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Mummunar Asara, Ƴan Majalisa 5 Sun Fice
  • Majalisar Wakilai Ta Dakatar Da CBN Daga Sallamar Ma’aikata 1000

Hakan nen ma ya sanya masharhanta da dama ke jinjinawa kwazon kasar a fannin yaki da fatara, musamman ta hanyar dunkule dabarun bunkasa ci gaban tattalin arziki, da manufofin inganta walwalar al’umma. Ta hanyar tsara manufofi daidai da yanayin da ake ciki a sassan kasar daban daban, kasar Sin ta tabbatar da ganin matakan yaki da fatara sun magance takamaiman matsalolin al’ummu mabambanta.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Wannan wani tsari ne da ya taimaka matuka, wajen sauya yanayin wasu sassan kasar da a baya suka yi fama da matsanancin kangin talauci, har ma hakan ya zama misali, kuma abun koyi ga kasashen duniya da dama a wannan fanni.

 

Ga misali, a kasar Rwanda, fasahar noman ciyawar Juncao da kasar Sin ta gabatar, ta taimakawa manoman yankunan karkara, da fasahar noman nau’o’in tsirrai kamar lemar kwado da ciyayin kiwata dabbobi. Hakan ya baiwa manoman kasar damar samun karin kudaden shiga, da samar da yalwar abinci, da tabbatar da ingancin muhalli. Yanzu haka wannan fasaha ta noman Juncao ta shiga kasashen nahiyar Afirka sama da 40, inda a ko ina ake cin gajiyarta.

 

Baya ga batun yaki da fatara, kasar Sin ta gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya” ko BRI, wadda da hadin kan sauran kasashe musamman masu tasowa ake samar da ababen more rayuwa, da raya ilimi da kiwon lafiya. Ko shakka babu wadannan ayyuka sun samar da guraben ayyukan yi, da hade sassa mabambanta wuri guda, da yaukaka ci gaban kowa da kowa, tare da taimakawa wajen tsamo dubban jama’a daga kangin fatara.

 

BRI ta riga ta hallara kasashe da yankunan duniya sama da 160, kana ana aiwatar da manufofinta masu inganci tare da sama da kasashen duniya 150, kuma karkashinta an shigar da kudaden da yawansu ya doshi dalar Amurka biliyan 20, don gudanar da ayyukan raya kasashe sama da 1,100. Wanda hakan ya zamo wata kyakkyawar dama ta ingiza ci gaban kasashe masu tasowa, da sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jam’iyyar Labour Ta Yi Mummunar Asara, Ƴan Majalisa 5 Sun Fice

Next Post

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

4 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

4 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

6 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

7 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

15 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

16 hours ago
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.