ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Fatara: Gudummawar Sin Da Tasirinta Tsakanin Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Fatara

Kudurin kawar da talauci na cikin muhimman bukatun bil adama da tun kaka da kakanni ake hankoron cimma nasararsa. Kuma a duniyar yau, akwai mutane da yawansu ya haura biliyan guda dake rayuwa cikin kangin talauci. Yayin da duniya ke kara dukufa wajen shawo kan wannan matsala, kasar Sin ta yi namijin kokari, wajen samar da damammaki na karfafa gwiwar al’ummun duniya don cimma kyakkyawar rayuwa.

 

A cikin gida, kasar Sin ta yi nasarar tsame sama da al’ummunta miliyan 800 daga kangin talauci, ta kuma yi nasarar cimma kudurin samar da ci gaba mai dorewa, wanda ke cikin ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan da shekarar 2030, tun ma kafin cikar wa’adin ajandar.

ADVERTISEMENT
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Mummunar Asara, Ƴan Majalisa 5 Sun Fice
  • Majalisar Wakilai Ta Dakatar Da CBN Daga Sallamar Ma’aikata 1000

Hakan nen ma ya sanya masharhanta da dama ke jinjinawa kwazon kasar a fannin yaki da fatara, musamman ta hanyar dunkule dabarun bunkasa ci gaban tattalin arziki, da manufofin inganta walwalar al’umma. Ta hanyar tsara manufofi daidai da yanayin da ake ciki a sassan kasar daban daban, kasar Sin ta tabbatar da ganin matakan yaki da fatara sun magance takamaiman matsalolin al’ummu mabambanta.

 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Wannan wani tsari ne da ya taimaka matuka, wajen sauya yanayin wasu sassan kasar da a baya suka yi fama da matsanancin kangin talauci, har ma hakan ya zama misali, kuma abun koyi ga kasashen duniya da dama a wannan fanni.

 

Ga misali, a kasar Rwanda, fasahar noman ciyawar Juncao da kasar Sin ta gabatar, ta taimakawa manoman yankunan karkara, da fasahar noman nau’o’in tsirrai kamar lemar kwado da ciyayin kiwata dabbobi. Hakan ya baiwa manoman kasar damar samun karin kudaden shiga, da samar da yalwar abinci, da tabbatar da ingancin muhalli. Yanzu haka wannan fasaha ta noman Juncao ta shiga kasashen nahiyar Afirka sama da 40, inda a ko ina ake cin gajiyarta.

 

Baya ga batun yaki da fatara, kasar Sin ta gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya” ko BRI, wadda da hadin kan sauran kasashe musamman masu tasowa ake samar da ababen more rayuwa, da raya ilimi da kiwon lafiya. Ko shakka babu wadannan ayyuka sun samar da guraben ayyukan yi, da hade sassa mabambanta wuri guda, da yaukaka ci gaban kowa da kowa, tare da taimakawa wajen tsamo dubban jama’a daga kangin fatara.

 

BRI ta riga ta hallara kasashe da yankunan duniya sama da 160, kana ana aiwatar da manufofinta masu inganci tare da sama da kasashen duniya 150, kuma karkashinta an shigar da kudaden da yawansu ya doshi dalar Amurka biliyan 20, don gudanar da ayyukan raya kasashe sama da 1,100. Wanda hakan ya zamo wata kyakkyawar dama ta ingiza ci gaban kasashe masu tasowa, da sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya.

Fatara
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Fatara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zababbiyar Shugabar Namibia

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.